Gabatarwa
Hasumiyar Tsaro Nuwamba–Disamba
“Muna nuna wa kowa a wannan unguwar Hasumiyar Tsaro. [Ka nuna bangon.] Wasu sun ɗauka cewa yin addu’a ɓata lokaci ne domin babu wanda ke jin addu’o’i. Wasu kuma sun yarda cewa Allah yana jin addu’o’insu. Mene ne ra’ayinka? [Ka bari ya ba da amsa.] Ka lura da abin da Littafi Mai Tsarki ya ce game da addu’a. [Karanta Ishaya 30:19.] Wannan mujallar ta ambata abubuwan da suka nuna cewa Allah yana ji da kuma amsa addu’o’in da aka yi a hanyar da ta dace kuma ta jitu da nufinsa.”
Awake! Nuwamba
“Miliyoyin mutane a faɗin duniya sun damu don munafunci da kuma koyarwar ƙarya da addinai dabam-dabam suke yi. Me kake ganin zai faru da addinai a nan gaba? [Ka bari ya ba da amsa.] Wannan mujallar ta tattauna wani annabci na musamman da ke littafin Ru’ya ta Yohanna da ta yi magana a kan yadda mutane a yau za su fito daga addinin ƙarya da kuma yadda za a halaka shi kwata-kwata.”