Gabatarwa
Don Soma Nazari da Mutane a Asabar ta Farko a Watan Nuwamba
“Don Allah ka ga wannan tambaya mai ban sha’awa. [Karanta tambaya ta farko a bangon baya na Hasumiyar Tsaro ta Nuwamba–Disamba.] Mece ce amsarka?” [Karanta sakin layi na farko a ƙarƙashin tambayar da kuma ɗaya daga cikin nassosin da ke wurin.] Ka ba shi mujallun kuma ka shirya don ka dawo ku tattauna sakin layi na gaba.
Hasumiyar Tsaro Nuwamba–Disamba
“Yau muna tattaunawa ne da maƙwabtanmu game da wani furucin da ke cikin sananniyar addu’ar da Yesu ya koya wa mabiyansa. [Karanta Matta 6:9, 10.] Shin ka taɓa samun bayani na ƙwarai a kan ma’anar Mulkin Allah da kuma dalilin da ya sa Yesu ya yi koyarwa sosai a kan Mulkin? [Ka bari ya ba da amsa.] Wannan mujallar tana ɗauke da abin da Littafi Mai Tsarki ya faɗa game da Mulkin Allah da kuma albarku masu yawa da Mulkin zai kawo a nan duniya.”
Awake! Nuwamba
“Kowa yana so ya yi farin ciki, amma mutane da yawa a yau ba sa yin hakan. Me kake ganin zai iya sa mutum farin ciki ƙwarai? [Ka bari ya ba da amsa.] Ni kaina na shaida yadda Littafi Mai Tsarki yake taimaka wa mutum ya kasance da farin ciki. Alal misali, ka yi la’akari da ƙa’idar da ke cikin wannan nassin. [Karanta Ibraniyawa 13:5.] Wannan mujallar ta bayyana abubuwa guda huɗu daga Littafi Mai Tsarki da za su iya sa mutum ya kasance da farin ciki.”