DARUSSA DAGA KALMAR ALLAH | FARAWA 15-17
Me Ya Sa Jehobah Ya Canja wa Ibram da Saraya Suna?
17:1, 3-5, 15, 16
Ibram mai adalci ne a gaban Jehobah. A lokacin da Jehobah ya yi musu alkawari, ya canja sunayensu zuwa wasu sunaye da ma’anarsu suka nuna abin da zai faru a nan gaba.
Kamar yadda ma’anar sunayensu suka nuna, Ibrahim ya zama baban al’umma da yawa, Saratu kuma ta zama mamar sarakuna.
Ibrahim
Baban Dubun-dubbai
Saratu
Sarauniya
Ko da yake ba mu muke zaɓan sunayen da za a ba mu ba, duk da haka, kamar Ibrahim da Saratu, za mu iya kasance da suna mai kyau ta yadda muke yin rayuwarmu. Ka tambayi kanka:
‘Me zan yi don in zama mai adalci a gaban Jehobah?’
‘Wane suna ne nake so Jehobah ya kira ni da shi?’