DARUSSA DAGA KALMAR ALLAH | FITOWA 23-24
Kada Ka Bi Bayan Taron Jama’a
23:1-3
Jehobah ya gargaɗi shaidu da alkalai cewa kada su bi taron jama’a wajen ba da shaidar ƙarya ko su yi son kai sa’ad da suke shari’a. Za mu iya bin gargaɗin a wasu fannonin rayuwarmu. Duniyar nan tana matsa wa Kiristoci su riƙa tunani da yin abubuwa yadda mutanen da ba su san Allah ba suke yi.—Ro 12:2.
Me ya sa bai kamata mu bi bayan taron jama’a sa’ad da
muka ji gulma ko jita-jita da ba mu tabbatar ba?
muke zaɓan tufafi da ado ko kuma nishaɗi ba?
muke sha’ani da mutanen da suka fito daga wata ƙasa ko ƙabila da masu kuɗi ko talakawa ba?