RAYUWAR KIRISTA
Ka Guje Wa Lalata Kamar Yadda Yusuf Ya Yi
Yusuf ya nuna mana abin da ya fi kyau mu yi sa’ad da ake matsa mana mu yi lalata. Yusuf yakan ƙi amincewa a duk lokacin da matar shugabansa ta so ta rinjaye shi ya kwana da ita. (Fa 39:7-10) Abin da ya gaya mata shi ne: “Don me zan yi wannan babbar mugunta, in yi wa Allah zunubi?” Kuma hakan ya nuna cewa Yusuf ya riga ya san cewa Jehobah ba ya so ma’aurata su ci amanar juna. Da matsin ya yi yawa, Yusuf ya gudu. Bai tsaya yana jani-in-jaka da ita ba domin hakan zai iya sa ya yi masa wuya ya guje mata.—Fa 39:12; 1Ko 6:18.
KU KALLI BIDIYON NAN KU GUJE WA LALATA, SA’AN NAN KU AMSA TAMBAYOYIN NAN:
Wane yanayi ne Jin ya fuskanta?
Waɗanne tambayoyi ne Jin ya yi wa kansa sa’ad da Mee-Kyong ta ce ya koya mata lissafi?
Yaya Jin ya ji game da abin da Mee-Kyong ta gaya masa?
Me ya taimaka wa Jin?
Mene ne Jin ya yi don ya guje wa lalata?
Waɗanne darussa ne ka koya daga bidiyon nan?