Tsarin Ayyuka na Makon 26 ga Oktoba
MAKON 26 GA OKTOBA
Waƙa ta 15 da Addu’a
Nazarin Littafi Mai Tsarki na Ikilisiya:
ia babin na 1 sakin layi na 1-13 (minti 30)
Makarantar Hidima ta Allah:
Karatun Littafi Mai Tsarki: 1 Labarbaru 12-15 (minti 8)
Bitar Makarantar Hidima ta Allah (minti 20)
Taron Hidima:
JIGON WATA: Ku zama “dasassu” da kuma ‘kafaffu cikin bangaskiya.’—Kol. 2:6, 7.
Waƙa ta 120
Minti 10: Littattafan da Za Mu Ba Mutane a Watan Nuwamba. Tattaunawa. Ka yi furucin da zai sa ‘yan’uwa su yi marmarin ba da warƙoƙi da kuma littafin nan Menene Ainihi Littafi Mai Tsarki Yake Koyarwa? Ka ɗan tattauna wasu bayanai da ke talifin nan “Sabon Tsari da Aka Yi ma Sababbin Warƙoƙi!” a Hidimarmu ta Mulki ta watan Afrilu 2014. Ka sa a yi gwajin da ya dace da yanayin mutanen yankinku.
Minti 20: “Kalmar Allah Tana Samun Iko a Rayuwarka Kuwa?” Jawabi. Bayan ka yi gajeriyar gabatarwa, ka saka wasan kwaikwayon nan “Kada Ka Karaya Sa’ad da Jehobah Ya Yi Maka Gyara!” da ke dandalin jw.org/ha. Ka ambata yadda yin bimbini a kan Kalmar Allah zai taimaka mana mu san wasu ƙa’idodin da za su amfane mu. Ka kammala jawabin ta wajen ƙarfafa ‘yan’uwa su riƙa sauraron wasan kwaikwayo daga Littafi Mai Tsarki da ke dandalin jw.org/ha don su amfana.
Waƙa ta 113 da Addu’a