Tsarin Ayyuka na Makon 24 ga Nuwamba
MAKON 24 GA NUWAMBA
Waƙa ta 50 da Addu’a
Nazarin Littafi Mai Tsarki na Ikilisiya:
cl babi na 16, sakin layi na 10-17 (minti 30)
Makarantar Hidima ta Allah:
Karatun Littafi Mai Tsarki: Kubawar Shari’a 28-31 (minti 10)
Na 1: Kubawar Shari’a 30:15–31:8 (minti 4 ko ƙasa da hakan)
Na 2: Wajibi Ne Dukan Kiristoci Su Zama Ministoci—td 31A (minti 5)
Na 3: Yadda Za A Faranta wa Allah Rai—lr babi na 40 (minti 5)
Taron Hidima:
Waƙa ta 47
Minti 10: “Ku Yi Amfani da Dandalinmu Sa’ad da Kuke Wa’azi—‘An Amsa Tambayoyin Littafi Mai Tsarki.’” Tattaunawa. Ka ambata wasu tambayoyi da aka ba da amsoshinsu a wannan sashen dandalinmu. (Ka shiga jw.org/ha, ƙarƙashin KOYARWAR LITTAFI MAI TSARKI > AN AMSA TAMBAYOYIN LITTAFI MAI TSARKI.) Ka sa a yi gwaji a kan ɗaya daga cikin shawarwarin da aka bayar a cikin talifin. Ka ba masu sauraro dama su faɗi wasu hanyoyi da za a iya yin amfani da wannan sashen dandalinmu sa’ad da suke wa’azi.
Minti 5: “Ban Sake Samunsa a Gida Ba!” Tattaunawa. Ka tattauna dalilin da ya sa ya kamata mu nace idan yana yi mana wuya mu sake samun wani da muka yi masa wa’azi a gida.—Mat. 28:19, 20; Mar. 4:14, 15; 1 Kor. 3:6.
Minti 15: “Wani Sabon Kayan Bincike.” Jawabi. Ka yi bitar umurnin da ke ƙarƙashin jigon nan “Yadda Za Ka Fara Bincike,” a gabatarwar littafin nan Littafin Bincike Don Shaidun Jehobah. Ka bayyana fasalolin wannan sabon littafin. Ka sa wani mai shela ya yi-wa-kansa-magana yayin da yake amfani da littafin.
Waƙa ta 69 da Addu’a