Watchtower LABURARE NA INTANE
Watchtower
LABURARE NA INTANE
Hausa
Ɓ
  • Ā
  • ā
  • Ɓ
  • ɓ
  • ɗ
  • Ɗ
  • Ƙ
  • ƙ
  • ꞌY
  • ꞌy
  • LITTAFI MAI TSARKI
  • WALLAFE-WALLAFE
  • TARO
  • ijwex talifi na 10
  • An Dauka Cewa Ni Ne Faston

Babu bidiyo don wannan zabin

Yi hakuri, bidiyon na da dan matsala

  • An Dauka Cewa Ni Ne Faston
  • Labarai
  • Makamantan Littattafai
  • Samun Gaskiya a Inda Ba Za a Yi Tsammani Ba
    Hasumiyar Tsaro Mai Shelar Mulkin Jehobah—2003
  • Albarkun Wa’azi da Amalanke a Fadin Duniya
    Littafin Taro Don Rayuwa ta Kirista da Hidimarmu—2018
  • Sakamakon Yin Murmushi!
    Hasumiyar Tsaro Mai Shelar Mulkin Jehobah (Na Nazari)—2021
Labarai
ijwex talifi na 10
Wasu mutane biyu suna magana da wani Mashaidi. Daya daga cikin mutane yana nuna wasu da mutane suka taru a makabartan don a ba da jawabi.

An Dauka Cewa Ni Ne Faston

Osman da matarsa da kuma diyarsa na wa’azi da amalanke a wajen wani makabarta a kasar Chile. Ba zato, sai ga jama’a da yawa masu raka gawa sun iso suna kadai-kadai. Sai wasu a cikinsu suka dauka Osman wani Fastonsu ne, sai suka yi kusa da shi suka rungume shi suka ce, “Mun gode da ka iso nan da wuri, Fasto, da ma kai muke jira!”

Ko da yake Osman ya yi kokari ya yi masu bayani, amma jama’a na surutu kuma hakan ya sa ba su fahimce shi ba. Bayan yan mintoci da jama’a suka shiga cikin makabarta, sai wasu su suka dawo wurin shi suka ce masa, “Fasto, muna jiranka a cikin makabartar.”

Da mutanen suka rage surutun, sai Osman ya sami damar gaya musu ko wane ne shi da kuma dalilin da yasa yake wurin. Bayan mutanen sun nuna fushinsu domin fastonsu bai zo ba, sai suka roke Osman suka ce: “Za ka iya shigowa ka yi wata karamin jawabi daga Littafi Mai Tsarki don mutanen da suka taru a makabartar?” Sai Osman ya amince ya yi hakan.

Sa’ad da suke hanyar zuwa wurin da aka haka kabarin, sai Osman ya yi masu tambayoyi game da mamacin, kuma ya yi tunanin nassosin da za su amfane mutanen. Da ya isa bakin kabari, sai ya gabatar da kansa wa jama’a kuma ya yi masu bayani cewa a matsayinsa na Mashaidin Jehobah, yana shelar bishara ga mutane.

Sai ya yi amfani Ru’ya ta Yohanna 21:​3, 4 da Yohanna 5:​28, 29 kuma ya yi bayyana cewa Allah bai halicci mutane don su rika mutuwa ba. Ya ce nan ba da dadewa ba Allah zai ta da matattu kuma za su samu damar yin rayuwa a duniya har abada. Da Osman ya kammala jawabin, sai mutane da yawa suka rungume shi suna murna kuma suka yi masa godiya domin wa’azin “sakon Jehobah” da ya yi musu. Sai ya koma wurin Amalanken wa’azin.

Da aka gama jana’izar, wasu a cikin masu makoki suka zo wurin amalanken wa’azi, suka tambaye Osman da iyalinsa tambayoyi game da Littafi Mai Tsarki. Bayan sun dau lokaci suna tattaunawa, sai suka karbi kusan duka mujallu da ke amalanken wa’azin.

    Littattafan Hausa (1987-2026)
    Fita
    Shiga Ciki
    • Hausa
    • Raba
    • Wadda ka fi so
    • Copyright © 2026 Watch Tower Bible and Tract Society of Pennsylvania
    • Ka'idojin Amfani
    • Tsarin Tsare Sirri
    • Saitin Tsare Sirri
    • JW.ORG
    • Shiga Ciki
    Raba