DARUSSA DAGA KALMAR ALLAH | FITOWA 37-38
Bagadai da Ke Mazauni da Amfaninsu a Bauta Ta Gaskiya
37:25, 29; 38:1
An gina bagadan daidai da yadda Jehobah ya faɗa kuma suna da muhimmanci.
Jehobah yana jin daɗin addu’o’in da bayinsa suke masa kamar yadda yake jin daɗin turaren ƙonawa
Jehobah yana karɓan hadayun da aka yi a bagaden ƙona hadayu. Yadda aka yi bagaden a gaban mazaunin, ya nuna mana cewa dole ne mu ba da gaskiya ga hadayar Yesu don Jehobah ya amince da mu.—Yoh 3:16-18; Ibr 10:5-10
Ta yaya za mu sa addu’armu ta zama kamar turare mai ƙamshi a gaban Allah?—Za 141:2