RAYUWAR KIRISTA
Ƙasar Ta “Shanye Ruwan Kogin”
A zamanin dā, hukumomin gwamnati sun taimaka wa bayin Jehobah. (Ezr 6:1-12; Es 8:10-13) Ko a yanzu ma, muna ganin yadda “ƙasar,” wato wasu hukumomi da suke da kirki a zamanin nan suke shanye “ruwan kogin” ko kuma dakatar da tsanantawa da “dodon” nan wato Shaiɗan yake sa a yi wa mutanen Allah. (R. Yar 12:16) A wasu lokuta, Jehobah, “Allah na ceto” yakan sa hukumomi su taimaka wa mutanensa.—Za 68:20; K. Ma 21:1.
Me za ka yi idan aka saka ka a fursuna don imaninka? Ka tabbata cewa Jehobah yana gani kuma zai kula da kai. (Fa 39:21-23; Za 105:17-20) Ban da haka ma, Jehobah zai albarkace ka don bangaskiyarka kuma amincinka zai ƙarfafa ’yan’uwa a faɗin duniya.—Fib 1:12-14; R. Yar 2:10.
KU KALLI BIDIYON NAN AN SAKI ’YAN’UWA DAGA GIDAN YARI A KORIYA, SAI KU AMSA TAMBAYOYI NA GABA:
Me ya sa an yi shekaru ana saka ’yan’uwanmu da yawa a fursuna a Koriya ta Kudu?
Wane mataki ne hukumomi suka ɗauka da ya sa aka sako ’yan’uwanmu tun lokacinsu bai yi ba?
Ta yaya za mu taimaka wa ’yan’uwanmu da suke fursuna domin imaninsu a faɗin duniya?
Ta yaya za mu yi amfani da ’yancin da muke da shi yanzu?
Waye yake taimaka mana mu yi nasara a shari’a da yawa da muke yi?
Ta yaya nake amfani da ’yancin da nake da shi?