RAYUWAR KIRISTA
Hanyoyin Kyautata Yadda Muke Wa’azi—Taimaka Ma Waɗanda Suke So Su Zama Mabiyan Yesu
MUHIMMANCINSA: Jehobah yana taimaka ma “waɗanda suke da zuciya ta samun rai na har abada” su zo su bauta masa. (A. M 13:48, New World Translation; 1Ko 3:7) Muna wannan aikin tare da shi ta wajen mai da hankali ga waɗanda suke aikata abin da suke koya. (1Ko 9:26) Muna bukatar mu taimaka musu su fahimci cewa wajibi ne su yi baftisma idan suna son su sami ceto. (1Bi 3:21) Mu taimaka wa ɗalibanmu su zama mabiyan Yesu ta wajen koya musu yadda za su gyara rayuwarsu da yin wa’azi da kuma keɓe kansu ga Jehobah.—Mt 28:19, 20.
YADDA ZA MU CIM MA HAKAN:
Ku tuna wa ɗalibanku cewa ainihin dalilin da ya sa kuke nazari da su shi ne don su “san” Jehobah kuma su faranta masa rai.—Yoh 17:3
Ku taimaka musu su daina halayen banza da kuma tarayya da abokan banza
Ku riƙa ƙarfafa su sosai kafin su yi baftisma da kuma bayan sun yi hakan.—A. M 14:22
KU KALLI BIDIYON NAN JEHOBAH ALLAH ZAI TAIMAKE KA, SAI KU AMSA TAMBAYOYIN NAN:
Mene ne zai iya sa mutum ya ji tsoron yin alkawarin bauta ma Jehobah kuma ya yi baftisma?
Ta yaya dattawa za su taimaka wa ɗaliban Littafi Mai Tsarki su sami ci gaba a ibadarsu?
Mene ne littafin Ishaya 41:10 ya koya mana game da Jehobah?
Waɗanne halaye ne za su taimaka mana mu bauta wa Jehobah da kyau duk da cewa mu ajizai ne?
Ta yaya muke yin aiki tare da Jehobah a wa’azi?