Tsarin Ayyuka na Makon 16 ga Nuwamba
MAKON 16 GA NUWAMBA
Waƙa ta 17 da Addu’a
❑ Nazarin Littafi Mai Tsarki na Ikilisiya:
ia babi na 2 sakin layi na 13-23, da tambayoyi don bimbini da ke shafi na 24 (minti 30)
Makarantar Hidima ta Allah:
Karatun Littafi Mai Tsarki: 1 Labarbaru 26-29 (minti 8)
Na 1: 1 Labarbaru 29:20-30 (minti 3 ko ƙasa da hakan)
Na 2: Mene Ne Kristi Zai Dawo Yi?—wp14 1/1 16 sakin layi na 1-4 (minti 5)
Na 3: Abin da Ya Sa Kiristoci na Gaskiya Suke Bin Gargaɗin da Ke Romawa 12:19 (minti 5)
Taron Hidima:
JIGON WATA: “Ni na dasa, Afollos ya yi ban ruwa; amma Allah ne ya ba da amfani.”—1 Kor. 3:6.
Waƙa ta 35
Minti 10: Ku Ci gaba da Yi wa Ɗalibanku “Ban Ruwa.” (1 Kor. 3:6-8) Ka gana da majagaba na kullum da kuma mai shela. Yaya suka tsara ayyukansu don su iya koma ziyara wajen waɗanda suka saurari saƙonmu? Waɗanne shirye-shirye suke yi? Yaya suke bi da ƙalubalen rashin samun mutanen a gida? Waɗanne labarai masu daɗi suka samu?
Minti 20: “Yadda Za Ku Yi Amfani da Sauti.” Tambayoyi ana ba da amsoshi. Ka bayyana yadda masu shela za su iya shiga sashen sauti a dandalinmu na jw.org/ha. Ka sa wa masu sauraro wani sauti su ji. Ka sa a sake yin gwaji da ke ƙarshen talifin nan “Ku Yi Amfani da Dandalinmu Sa’ad da Kuke Wa’azi—‘An Amsa Tambayoyin Littafi Mai Tsarki’” a Hidimarmu ta Mulki ta Nuwamba, 2014.
Waƙa ta 108 da Addu’a