Tsarin Ayyuka na Makon 19 ga Oktoba
MAKON 19 GA OKTOBA
Waƙa ta 54 da Addu’a
Nazarin Littafi Mai Tsarki na Ikilisiya:
ia shafi na 2-3 da kuma gabatarwa, sakin layi na 1-15 (minti 30)
Makarantar Hidima ta Allah:
Karatun Littafi Mai Tsarki: 1 Labarbaru 8-11 (minti 8)
Na 1: 1 Labarbaru 11:15-25 (minti 3 ko ƙasa da hakan)
Na 2: Ta Yaya Addu’o’in da Jehobah Yake Ji Suna Kama da Turare Mai Ƙamshi a Gabansa?—Zab. 141:2; R. Yoh. 5:8 (minti 5)
Na 3: Mene Ne Ya Wajaba Mu Yi don Allah Ya Saurare Mu?—wp13 9/1 16 sakin layi na 1-4 (minti 5)
Taron Hidima:
JIGON WATA: Ku zama “dasassu” da kuma ‘kafaffu cikin bangaskiya.’—Kol. 2:6, 7.
Waƙa ta 83
Minti 20: “Yadda Za Mu Ratsa Zukatan Mutane.” Tambayoyi ana ba da amsoshi. Ka sa a yi gwaji biyu da suka bambanta da juna. Wata mata ta gaya wa mai shela cewa yaronta ya mutu kuma yana sama yanzu. A gwaji na farko, mai shelan ya karanta littafin Mai-Wa’azi 9:5 da ya yi magana game da yanayin matattu. Matar ba ta gamsu da ayar ba kuma ta yi banza da maganar. A gwaji na biyu, mai shelan da basira ya karanta littafin Yohanna 5:28, 29 da ya yi magana game da begen tashin matattu kuma bayan haka, matar ta saurari saƙon da zuciya ɗaya.
Minti 10: Yara da Manya, Ku Kafa wa Wasu Misali Mai Kyau. (Filib. 3:17; 1 Tim. 4:12) Tattaunawar da aka ɗauko daga Hasumiyar Tsaro ta 15 ga Maris, 2015, shafi na 6 sakin layi na 2-3 da kuma 15 ga Maris, 2013, shafi na 32 sakin layi na 1-5. Ka ba masu sauraro dama su faɗi darussan da suka koya.
Waƙa ta 90 da Addu’a