Tsarin Ayyuka na Makon 20 ga Janairu
MAKON 20 GA JANAIRU
Waƙa ta 34 da Addu’a
□ Nazarin Littafi Mai Tsarki na Ikilisiya:
cl babi na 1 sakin layi na 18-23 da akwati a shafi na 14 (minti 30)
□ Makarantar Hidima ta Allah:
Karatun Littafi Mai Tsarki: Farawa 11-16 (minti 10)
Na 1: Farawa 14:17–15:11 (minti 4 ko ƙasa da hakan)
Na 2: Ba Za A Taɓa Daina Rayuwa a Duniya Ba—td 15B (minti 5)
Na 3: Wanda Ya Halicci Dukan Abubuwa—lr babi na 3 (minti 5)
□ Taron Hidima:
Waƙa ta 123
Minti 10: Mene Ne Muka Koya? Tattaunawa. Ka sa a karanta Matta 7:6-11. Ka tattauna yadda wannan nassin zai taimaka mana a wa’azi.
Minti 10: Ku Girmama Waɗanda Suke Aiki Tuƙuru a Tsakaninku. (1 Tas. 5:12, 13) Tattaunawa ta wajen yin amfani da tambayoyin da ke gaba: (1) A waɗanne hanyoyi ne dattawa suke aiki tuƙuru a cikin ikilisiya? (2) Ta yaya za mu nuna cewa muna daraja dattawa sosai? (3) Me ya sa dattawa suke bukatar ƙarfafa? (4) A waɗanne hanyoyi ne za mu iya ƙarfafa dattawa da kuma iyalansu? (5) Idan muka yi biyayya ga dattawa, ta yaya dattawan da kuma ikilisiyar baki ɗaya za su amfana?
Minti 10: “Ku Taimaki Wanda Kuka Fita Wa’azi Tare.” Tambayoyi ana ba da amsoshi. Ka ba masu sauraro dama su faɗi abin da suka koya daga wani da suka taɓa fita wa’azi tare.
Waƙa ta 93 da Addu’a