Bitar Makarantar Hidima ta Allah
Za a amsa waɗannan tambayoyi na gaba a Makarantar Hidima ta Allah a makon 26 ga Agusta, 2013. An saka kwanan watan da za a tattauna waɗannan bayanan ne domin ku yi bincike sa’ad da kuke shiri don makaranta a kowane mako.
1. Wane darasi ne za mu koya daga Sarki Hirudus a yadda ya yarda mutane su ba shi daraja da kuma yabo da ba su dace da shi ba? (A. M. 12:21-23) [1 ga Yuli, w08 5/15 shafi na 32, sakin layi na 7]
2. Wane amfani ne Kiristoci matasa za su iya more daga yin nazari a kan labarin Timotawus da kuma bin misalinsa? (A. M. 16:1, 2) [8 ga Yuli, w08 5/15 shafi na 32, sakin layi na 10]
3. Ta yaya Biriskilla da Akila suka taimaka wa Afolos bayan sun saurare shi sa’ad da yake yin ‘magana da gaba gaɗi’ a cikin majami’a a Afisus? (A. M. 18:24-26) [15 ga Yuli, w10 6/15 shafi na 11, sakin layi na 4]
4. Wane sadaukarwa ne manzo Bulus ya yi don bishara? (A. M. 22:3) [22 ga Yuli, w09 9/15 shafi na 24 sakin layi na 13]
5. Mene ne keɓe kai ga Allah yake nufi? (A. M. 27:22-24) [29 ga Yuli, w10 1/15 shafi na 3 sakin layi na 2]
6. Ta yaya mutane da yawa a yau suke nuna rashin daraja ga aure da kuma Jehobah Allah? (Rom. 1:24-32) [5 ga Agusta, w11 1/15 shafi na 13 sakin layi na 3]
7. Ta yaya “fansa da . . . Yesu Kristi” ya biya a shekara ta 33 a zamaninmu ta share ‘zunuban’ mutanen dā kafin a biya ta? (Rom. 3:24, 25) [5 ga Agusta, w08 6/15 shafi na 29, sakin layi na 6]
8. Wane tanadi ne Jehobah ya yi don ya taimaka mana sa’ad da muke fuskantar wani yanayi mai tsanani sosai har ba mu san takamaiman abin da za mu ambata a addu’armu ba? (Rom. 8:26, 27) [12 ga Agusta, w08 6/15 shafi na 30 sakin layi na 10]
9. Mene ne Littafi Mai Tsarki yake nufi sa’ad da ya ba da umurni cewa mu riƙa karɓan “baƙi”? (Rom. 12:13) [19 ga Agusta, w09 10/15 shafi na 5 sakin layi na 12-13]
10. Ta yaya za mu bi “halin Ubangiji Yesu Almasihu,” kamar yadda manzo Bulus ya shawarta? (Rom. 13:14) [26 ga Agusta, w05 1/1 shafuffuka na 23-24 sakin layi na 20-22]