Tsarin Ayyuka na Makon 22 ga Afrilu
MAKON 22 GA AFRILU
Waƙa ta 85 da Addu’a
□ Nazarin Littafi Mai Tsarki na Ikilisiya:
wt babi na 4, sakin layi na 1-9 (minti 30)
□ Makarantar Hidima ta Allah:
Karatun Littafi Mai Tsarki: Luka 18-21 (minti 10)
Na 1: Luka 18:18-34 (minti 4 ko ƙasa da hakan)
Na 2: Mene Ne Yesu Yake Nufi Sa’ad da Ya Ce, “Ni da Ubana Ɗaya Ne”?—td 16C (minti 5)
Na 3: Mene Ne Tawali’u, Ta Yaya Za Mu Biɗe Shi Kuma Me Ya Sa Yake da Muhimmanci?—Zeph. 2:2, 3 (minti 5)
□ Taron Hidima:
Waƙa ta 125
Minti 10: Idan Wani Ya Ce, ‘Kafin Ka Yi Mini Wa’azi, Sai Ka Yi Addu’a.’ Tattaunawa. Ka yi amfani da tambayoyin da ke gaba wajen tattaunawa da masu sauraro: (1) Mene ne Yesu ya faɗa game da yin addu’a a idon jama’a don neman yabo? (Mat. 6:5) (2) Yaya ne Yesu ya ce ya kamata almajiransa su yi wa’azi? (Mat. 10:12, 13) (3) Mene ne Yesu ya ce almajiransa su yi sa’ad da suke shiga gidajen mutane don su yi wa’azi? (Mat. 10:7) (4) Ta yaya za mu daidaita tattaunawar don ta jitu da batun Mulkin Allah? (Mat. 6:9, 10; R. Yoh. 21:4) Ka sa a nuna yadda za a iya ba da amsa ga tambayar nan, ‘Me ya sa ba ku yin addu’a?’
Minti 20: Matakan da Za Ku Ɗauka don Ku Guje wa Waɗanda Suke Sace Mutane. Ka tattauna bayanin da ke wasiƙar 28 ga Oktoba, 2010, da aka aika zuwa ga dukan ikilisiyoyi. Ka tabbata cewa ka karanta ayoyin da aka ce a karanta a cikin wasiƙar kuma ka ba masu sauraro dama su faɗi yadda za su iya amfani da ayoyin da aka karanta.
Waƙa ta 70 da Addu’a