Ayyuka na Makon 30 ga Afrilu
MAKON 30 GA AFRILU
Waƙa ta 125 da Addu’a
□ Nazarin Littafi Mai Tsarki na Ikilisiya:
cl shafi na 171 zuwa 176 (minti 25)
□ Makarantar Hidima Ta Allah:
Karatun Littafi Mai Tsarki: Irmiya 32-34 (minti 10)
Bitar Makarantar Hidima Ta Allah (minti 20)
□ Taron Hidima:
Waƙa ta 82
Minti 10: Sanarwa. Ka yi amfani da minti ɗaya ko biyu wajen ambata wasu cikin talifofin da ke Hasumiyar Tsaro ta Afrilu-Yuni da kuma Awake! na Mayu da mutane a yankinku za su so. Bayan haka, ka ba ’yan’uwa damar su faɗi tambayar da za su yi wadda za ta sa mutane su yi sha’awar batun da suke son su tattauna da kuma nassin da za su karanta wanda ya yi daidai da kan maganar da ke bangon mujallun. Ka sa a gwada yadda za a iya ba da kowanne cikin mujallun.
Minti 15: Mene Ne Muka Koya? Tattaunawa. Ka sa a karanta Ayyukan Manzanni 4:1-13, 18-20. Ka tattauna yadda wannan labarin zai taimaka mana sa’ad da muke wa’azi.
Minti 10: “Anini Biyu.” Jawabi.
Waƙa ta 126 da Addu’a