22 ga Maris, 2008—Rana da Za a Tuna da Ita
Adaren mutuwarsa, Yesu ya ba da gurasa marar-yisti da kuma ruwan anab ga manzanninsa ya umurce su su ci su sha. Kuma ya gaya musu: “Ku yi wannan abin tunawa da ni.”—Luka 22:19.
A wannan shekarar tuna wannan aukuwa ya faɗi a ranar Asabar, 22 ga Maris, 2008. Shaidun Jehobah a dukan duniya za su taru a wannan dare na musamman don su Tuna Mutuwar Yesu a hanyar da ya umurta. Muna gayyatarka. Ka tambayi Shaidun Jehobah da suke kusa da kai don ka san ainihin wurin taron da kuma lokacinsa.