Watchtower LABURARE NA INTANE
Watchtower
LABURARE NA INTANE
Hausa
Ɓ
  • Ā
  • ā
  • Ɓ
  • ɓ
  • ɗ
  • Ɗ
  • Ƙ
  • ƙ
  • ꞌY
  • ꞌy
  • LITTAFI MAI TSARKI
  • WALLAFE-WALLAFE
  • TARO
  • lfb darasi na 101 p. 234-p. 235 par. 4
  • An Tura Bulus Kasar Roma

Babu bidiyo don wannan zabin

Yi hakuri, bidiyon na da dan matsala

  • An Tura Bulus Kasar Roma
  • Darussa daga Littafi Mai Tsarki
  • Makamantan Littattafai
  • Ka Yi Ƙarfin Zuciya, Jehobah Zai Taimake Ka
    Hasumiyar Tsaro Mai Shelar Mulkin Jehobah (Na Nazari)—2020
  • Bulus Ya Je Roma
    Littafin Taro Don Rayuwa ta Kirista da Hidimarmu—2019
  • Bishara Ta Yaɗu
    Littafi Mai Tsarki​—Wane Saƙo Ne Ke Cikinsa?
Darussa daga Littafi Mai Tsarki
lfb darasi na 101 p. 234-p. 235 par. 4
Bulus da sauran mutanen sun yi iyo, wasu kuma sun rike katakon jirgin da ya rushe zuwa gabar tekun Malita

DARASI NA 101

An Tura Bulus Ƙasar Roma

Sa’ad da Bulus yake zagaya ƙasashe dabam-dabam yana wa’azi a ƙaro na uku, an kama shi a Urushalima. Da aka kama shi, sai aka saka shi cikin kurkuku. Da daddare, Yesu ya gaya masa a wahayi cewa: ‘Za ka je Roma kuma ka yi wa’azi a wajen.’ An ɗauki Bulus daga Urushalima zuwa Kaisariya inda ya yi shekara biyu a kurkuku. Sa’ad da wani Gwamna mai suna Fastos yake saurarar ƙararsa, sai Bulus ya ce: ‘Ina son Kaisar ya hukunta ni a Roma.’ Sai Fastos ya ce: “To, ka nema a ɗaukaka ƙararka gaban Kaisar! Gun Kaisar kuwa za ka tafi.” Sai aka saka Bulus da wasu Kiristoci guda biyu masu suna Luka da Aristarkus a cikin jirgin ruwa don su je Roma.

Yayin da suke wannan tafiyar, an yi kwanaki da yawa ana iska mai ƙarfi. Kowa a jirgin ya zata zai mutu. Amma Bulus ya ce musu: ‘Wani mala’ika ya gaya mini a mafarki cewa: “Kada ka ji tsoro Bulus. Za ka kai Roma kuma babu abin da zai same ku.” Don haka, kada ku ji tsoro! Ba za mu mutu ba.’

An yi kwana 14 ana wannan iskar mai ƙarfi. A ƙarshe, sai suka zo kusa da ƙasar Malita. Jirgin ya bugi ƙasa kuma ya rugurguje gabaki ɗaya. Amma duka mutanen guda 276 sun tsira. Wasu sun yi iyo, wasu kuma sun riƙe katakon jirgin har suka isa bakin kogin. Mutanen da ke Malita sun kula da su sosai kuma suka hura wuta don su ji ɗumi.

Bayan wata uku, sai sojojin suka shiga wani jirgi tare da Bulus zuwa Roma. Sa’ad da ya kai, ’yan’uwa sun zo wurinsa. Da Bulus ya gan su, sai ya gode wa Jehobah kuma ya sami ƙarfin gwiwa. Ko da yake Bulus fursuna ne, an yarda ya zauna a gidan haya kuma soja ya riƙa gadinsa. Ya yi shekara biyu a wajen. Mutane suna zuwa wurinsa kuma yana musu wa’azi game da Mulkin Allah da kuma Yesu. Bulus ya rubuta wa ikilisiyoyin da ke Asiya Ƙarami da Yahudiya wasiƙu. Babu shakka, Jehobah ya sa Bulus ya yi wa mutane da yawa wa’azi.

“A cikin kowace matsala mu koɗa kanmu masu-hidimar Allah, cikin haƙuri mai-yawa, cikin ƙunci, cikin bukata, cikin matsuwa.”​—⁠2 Korintiyawa 6:4

Tambayoyi: Me ya sa Fastos ya tura Bulus Roma? Mene ne ya faru da Bulus sa’ad da yake zuwa Roma?

Ayyukan Manzanni 21:30; 23:11; 25:​8-12; 27:1–28:31; Romawa 15:​25, 26

    Littattafan Hausa (1987-2026)
    Fita
    Shiga Ciki
    • Hausa
    • Raba
    • Wadda ka fi so
    • Copyright © 2026 Watch Tower Bible and Tract Society of Pennsylvania
    • Ka'idojin Amfani
    • Tsarin Tsare Sirri
    • Saitin Tsare Sirri
    • JW.ORG
    • Shiga Ciki
    Raba