Watchtower LABURARE NA INTANE
Watchtower
LABURARE NA INTANE
Hausa
Ɓ
  • Ā
  • ā
  • Ɓ
  • ɓ
  • ɗ
  • Ɗ
  • Ƙ
  • ƙ
  • ꞌY
  • ꞌy
  • LITTAFI MAI TSARKI
  • WALLAFE-WALLAFE
  • TARO
  • bm sashe na 23 p. 26
  • Bishara Ta Yaɗu

Babu bidiyo don wannan zabin

Yi hakuri, bidiyon na da dan matsala

  • Bishara Ta Yaɗu
  • Littafi Mai Tsarki​—Wane Saƙo Ne Ke Cikinsa?
  • Makamantan Littattafai
  • Ka Yi Ƙarfin Zuciya, Jehobah Zai Taimake Ka
    Hasumiyar Tsaro Mai Shelar Mulkin Jehobah (Na Nazari)—2020
  • Ya Kāre Imaninsa a Gaban Manyan Sarakuna
    Hasumiyar Tsaro Mai Shelar Mulkin Jehobah (Na Nazari)—2016
  • An Tura Bulus Kasar Roma
    Darussa daga Littafi Mai Tsarki
  • Mutane da Yawa Sun Zama Kiristoci
    Darussa daga Littafi Mai Tsarki
Dubi Ƙari
Littafi Mai Tsarki​—Wane Saƙo Ne Ke Cikinsa?
bm sashe na 23 p. 26

Sashe 23

Bishara Ta Yaɗu

Bulus ya yi tafiye-tafiye na yin wa’azi a kan ƙasa da teku

BAYAN ya zama mabiyi, Bulus ya yi wa’azin bisharar Mulkin Allah da ƙwazo, kuma hakan ya sa wannan ɗan hamayya a dā ya fuskanci muguwar hamayya. Wannan manzo mai ƙwazo ya tafi wurare masu yawa don ya yi wa’azi, ya yi tafiya zuwa wurare masu nisa don ya yaɗa bishara game da Mulkin da zai cika ainihin manufar Allah ga ’yan Adam.

A lokaci na farko da ya fita yin wa’azi a Listra, Bulus ya warkar da wani mutumi da aka haifa gurgu. Sai mutane suka soma ihu suna cewa Bulus da abokin tafiyarsa Barnaba, alloli ne. Da kyar Bulus da Barnaba suka hana mutanen yin hadayu a gare su. Domin maƙiyan Bulus sun rinjaye su, sai waɗannan mutanen suka yi ta jifan Bulus da dutse har sa’ad da suka ɗauka cewa ya mutu. Bulus ya tsira daga wannan harin kuma bayan haka ya koma birnin don ya ƙarfafa almajiran da kalamai masu ƙarfafawa.

Wasu Yahudawa Kiristoci suna gardama cewa masu bi da ba Yahudawa ba suna bukatan su bi wasu ɓangarorin Dokar Musa. Bulus ya kai batun ga manzanni da dattawan da ke Urushalima. Bayan sun bincika Nassosi dalla-dalla da kuma ja-gorancin ruhu mai tsarki na Allah, waɗannan mutanen suka rubuta wasiƙa ga ikilisiyoyi kuma suka gargaɗe su su guji bautar gumaka, cin jini da dabbar da ba a yanka ba, da kuma zina. Waɗannan dokokin “wajibai” ne, amma bin su ba ya bukatan bin Dokar Musa.—Ayyukan Manzanni 15:28, 29.

A tafiyarsa ta biyu na yin wa’azi, Bulus ya ziyarci Biriya, wato, Helas na zamani. Yahudawan da ke wurin sun karɓi saƙon da hannu biyu-biyu, suna bincika Nassosi a kullum don su tabbatar da koyarwarsa. A nan kuma, hamayya ta tilasta masa ya tafi Atina. A gaban ’yan Atina masu ilimi sosai, Bulus ya ba da jawabi mai ƙarfi wanda misali ne mai kyau na amfani da basira, fahimi, da fasahar magana.

Bayan tafiya na uku na yin wa’azi, Bulus ya tafi Urushalima. Sa’ad da ya ziyarci haikalin da ke wurin, sai wasu Yahudawa suka ta da hargitsi, suna son su kashe shi. Sojojin Roma suka shiga tsakaninsu kuma suka yi wa Bulus tambayoyi. A matsayin ɗan ƙasar Roma, ya kāre kansa a gaban Gwamna Filikus ɗan Roma. Yahudawan sun kasa gabatar da wata shaida a kan tuhumar da suke yi wa Bulus. Don ya hana Fastos, wanda wani gwamna ne ɗan ƙasar Roma, ya miƙa shi ga Yahudawa, sai Bulus ya ce: “Na ɗaukaka roƙo zuwa wurin Kaisar.” Sai Fastos ya ce: “Wurin Kaisar za ka tafi.”—Ayyukan Manzanni 25:11, 12.

Daga nan sai aka ɗauki Bulus a cikin jirgin ruwa zuwa ƙasar Italiya don ya fuskanci shari’a. Domin jirgin ruwan ya yi haɗari, hakan ya sa lokacin ɗari ya same shi a tsibirin Malita. Sa’ad da ya isa ƙasar Roma, ya yi shekara biyu a gidan haya. Ko da yake sojoji suna gadinsa, wannan manzo mai ƙwazo ya ci gaba da yin wa’azin Mulkin Allah ga dukan waɗanda suka ziyarce shi.

—An ɗauko daga Ayyukan Manzanni 11:22–28:31.

◼ Menene ya faru bayan da Bulus ya warkar da wani gurgu a Listira?

◼ Ta yaya aka daidaita tambayar da aka yi game da bin Dokar Musa?

◼ Ta yaya ne Bulus ya sami kansa a Roma, kuma menene ya yi sa’ad da yake wurin?

[Taswira a shafi na 26]

Farawa

Fitowa

Levitikus

Littafin Lissafi

Kubawar Shari’a

Joshua

Alƙalawa

Ruth

1 Sama’ila

2 Sama’ila

1 Sarakuna

2 Sarakuna

1 Labarbaru

2 Labarbaru

Ezra

Nehemiya

Esther

Ayuba

Zabura

Misalai

Mai-Wa’azi

Waƙar Waƙoƙi

Ishaya

Irmiya

Makoki

Ezekiel

Daniyel

Hosiya

Joel

Amos

Obadiya

Yunana

Mikah

Nahum

Habakkuk

Zafaniya

Haggai

Zakariya

Malakai

Matta

Markus

Luka

Yohanna

● Ayyukan Manzanni

Romawa

1 Korintiyawa

2 Korintiyawa

Galatiyawa

Afisawa

Filibiyawa

Kolosiyawa

1 Tasalonikawa

2 Tasalonikawa

1 Timotawus

2 Timotawus

    Littattafan Hausa (1987-2026)
    Fita
    Shiga Ciki
    • Hausa
    • Raba
    • Wadda ka fi so
    • Copyright © 2026 Watch Tower Bible and Tract Society of Pennsylvania
    • Ka'idojin Amfani
    • Tsarin Tsare Sirri
    • Saitin Tsare Sirri
    • JW.ORG
    • Shiga Ciki
    Raba