DARUSSA DAGA KALMAR ALLAH | AYYUKAN MANZANNI 19-20
“Ku Lura da Kanku, da Kuma Dukan Garken”
Dattawa sun san cewa Kristi ya fanshi kowane Kirista da jininsa mai tamani, shi ya sa sukan ciyar da tumakin Kristi da kāre su da kuma kula da su. ’Yan’uwa a ikilisiya kuma, suna godiya da kuma ƙaunar dattawa domin yadda suke a shirye su taimaka ma ’yan’uwansu kamar yadda Bulus ya yi.