Ƙa’idar Ja-gora—Tana da Muhimmanci
Ko da yake yawancin mutane suna ganin Ƙa’idar Ja-Gora koyarwar ɗabi’a ce da Yesu ya ƙirƙiro, amma shi kansa ya ce: “Abin da ni ke koyarwa ba nawa ba ne, amma nasa ne wanda ya aiko ni.”—Yohanna 7:16.
HAKIKA, Tushen abin da Yesu ya koyar, har da abin da aka sani da Ƙa’idar Ja-Gora, wanda ya aiko Yesu ne, wato, Mahalicci, Jehovah Allah.
Asali, Allah ya nufi dukan mutane su bi da juna kamar yadda suke so a bi da su. A kafa misali mafi kyau na nuna damuwa da rayuwar wasu a yadda ya halicci mutane: “Allah fa ya halitta mutum cikin suratasa, cikin surar Allah ya halicce shi; na miji da ta mata ya halicce su.” (Farawa 1:27) Wannan yana nufin cewa Allah cikin ƙauna ya bai wa mutane kaɗan cikin shahararrun halayensa saboda su more rayuwa cikin salama, farin ciki, da jituwa—har abada. Lamiri da Allah ya ba su, idan suka koyar da shi da kyau, zai yi musu ja-gora su bi da wasu yadda su kansu za su so wasu su bi da su.
Son Kai Ya Ci Gari
Tun da mutane sun samu irin wannan mafari mai ban sha’awa, me ya faru? Son kai ya fito da mummunan kansa. Mutane da yawa suna sane da tarihin Littafi Mai Tsarki game da abin da ma’aurata na farko suka yi, kamar yadda yake rubuce a Farawa sura 3. Shaiɗan, ɗan hamayya ne da dukan mizanan adalci na Allah, ya zuga Adamu da Hawa’u, cikin son kai suka ƙi sarautar Allah suka gwammace ’yancin kansu da kuma dogara da kansu. Son kansu da kuma tawaye ya kai ga rashi wa kansu da kuma bala’i ga dukan zuriyarsu na gaba. Wannan misali na sarai na sakamakon ƙin koyarwa da aka san ta da Ƙa’idar Ja-Gora ne. Saboda haka, “zunubi ya shigo cikin duniya ta wurin mutum ɗaya, mutuwa kuwa ta wurin zunubi; har fa mutuwa ta bi kan dukan mutane, da shi ke duka sun yi zunubi.”—Romawa 5:12.
Ko da yake dukan ’yan Adam suna ƙin hanyoyin Jehovah Allah, bai yasar da su ba. Alal misali, Jehovah ya bai wa al’ummar Isra’ila Doka ta yi musu ja-gora. Ta koya musu su yi wa wasu kamar yadda su kansu suke so wasu su yi musu. Dokar ta ba da umurni game da yadda za a bi da bayi, marayu, da kuma gwauraye. Ta ba da umurni game da yadda za a bi da wulakanci, sace mutum, da kuma sata. Dokokin tsabta sun nuna damuwa ga lafiyar wasu. Da dokoki ma game da batutuwan jima’i. Jehovah ya taƙaice Dokarsa wajen gaya wa mutanen: ‘Ku yi ƙaunar maƙwabcinku kamar ranku,’ furci da Yesu ya ɗauko daga baya. (Leviticus 19:18; Matta 22:39, 40) Dokar kuma tana ɗauke da umurni game da yadda za a bi da baƙi da suke tsakanin Isra’ilawa. Dokar ta ba da umurni: “Ba za ka nuƙurƙusa baƙo ba: gama kun san halin baƙonci, da shi ke kuka yi baƙonci cikin ƙasar Masar.” Watau, Isra’ilawan ya kamata su yi kirki domin tausayin gajiyayyu.—Fitowa 23:9; Leviticus 19:34; Kubawar Shari’a 10:19.
Da zarar Isra’ilawan sun bi Dokar cikin aminci Jehovah ya albarkaci al’ummar. A lokacin sarautar Dauda da Sulemanu, al’ummar ta samu cin gaba kuma mutanen sun samu farin ciki da kuma wadata. Tarihi ya ce: “Yahuda da Isra’ila suna dayawa, misalin yashi a bakin teku domin yawa; suna ci, suna sha, suna ta nishatsi. Yahuda da Isra’ila suka zauna lafiya, kowane mutum ƙarƙashin kuringar anab nasa da itacen ɓaurensa.”—1 Sarakuna 4:20, 25.
Abin baƙin ciki, salama da kwanciyar rai na al’ummar bai daɗe ba. Ko da yake suna da Dokar Allah, Isra’ilawa ba su bi ta ba; sun ƙyale son kai ya cunkushe damuwarsu da wasu. Wannan, tare da ridda, ya jawo musu wahala ɗaɗɗaya kuma da dukan al’ummar. A ƙarshe, a shekara ta 607 K.Z., Jehovah ya ƙyale Babiloniyawa suka halaka sarautar Yahuda, da birnin Urushalima, har da haikali mai ban mamaki da yake can. Don me? “Tun da ba ku ji maganata ba, ga shi, sai in aike in ɗauki dukan kabilan arewa, in ji Ubangiji, da Nebuchadrezzar sarkin Babila, bawana, in kawo su su yi yaƙi da wannan ƙasa da mazaunanta, da dukan al’ummai na wajen nan; in halaka su sarai, in maishe su abin al’ajibi, abin reni, kufai har abada kuma.” (Irmiya 25:8, 9) Sakamakon yasar da tsarkakkiyar bauta ta Jehovah ke nan!
Misalin da Za a Yi Koyi da Shi
A wani ɓangare, Yesu bai koyar da Ƙa’idar Ja-Gora kawai ba, amma kuma ya ba da misali mafi kyau na bin ta. Ya damu da lafiyar wasu da gaske. (Matta 9:36; 14:14; Luka 5:12, 13) Sau ɗaya, a kusa da birnin Nayin, Yesu ya ga gwauruwa tana baƙin ciki a wajen jana’izar ɗanta makaɗaici. Labarin Littafi Mai Tsarki ya ce: “Sa’anda Ubangiji ya gan ta, ya yi juyayi bisa gareta.” (Luka 7:11-15) Furcin nan “ya yi juyayi,” in ji Vine’s Expository Dictionary of Old and New Testament Words, yana nufin “yin juyayi kamar ga kanka.” Ya ji zafin a zuciyarsa, kuma ya motsa shi ya yi ƙoƙari ya sauƙaƙa mata baƙin cikinta. Alal ya faranta ma wannan gwauruwar rai sa’ad da Yesu ya ta da yaro mamacin ya “bada shi ga uwatasa”!
A ƙarshe, cikin jituwa da nufin Allah, Yesu cikin son rai ya wahala kuma ya ba da ransa fansa saboda ’yan Adam su samu ’yanci daga bauta na zunubi da mutuwa. Wannan shi ne misali mafi girma na rayuwa bisa Ƙa’idar Ja-Gora.—Matta 20:28; Yohanna 15:13; Ibraniyawa 4:15.
Mutane da Suke Amfani da Ƙa’idar Ja-Gora
Da akwai mutane a zamaninmu da suke rayuwa bisa Ƙa’idar Ja-Gora da gaske? Hakika kuwa, kuma ba kawai a lokacin da yake da sukuni ba ne. Alal misali, lokacin Yaƙin Duniya na Biyu a Nazi na Jamus, Shaidun Jehovah sun riƙe bangaskiyarsu ga Allah da kuma ƙaunarsu ga maƙwabtansu kuma suka ƙi su yi ridda ga Ƙa’idar Ja-Gora. Yayin da Gwamnati ta tsananta nuna ƙiyayya da kuma wariya ga dukan Yahudawa, Shaidun sun ci gaba da bin Ƙa’idar Ja-Gora. Har a cikin sansanin fursuna, sun ci gaba da kula da ’yan’uwansu ’yan Adam, suna raba abincinsu, ko da yake ana ƙarancinsa, da Yahudawa da waɗanda ba Yahudawa ba da suke mutuwa don yunwa. Bugu da ƙari, ko da yake Gwamnati ta umurce su su ɗauki makamai su kashe wasu, sun ƙi su yi haka, kamar yadda ba sa so wasu su kashe su. Yaya za su kashe waɗanda ya kamata su ƙaunace su kamar ransu? Domin sun ƙi, da yawa cikinsu an kai su ba ga sansanin fursuna ba kawai har ga mutuwarsu.—Matta 5:43-48.
Yayin da kake karanta wannan talifin, kana amfana daga wani misali na yin amfani da Ƙa’idar Ja-Gora. Shaidun Jehovah sun fahimci cewa a yau mutane da yawa suna wahala babu wani bege ko taimako. Domin wannan, Shaidun suka ba da kansu da son rai su taimake wasu su koya game da bege da kuma ja-gora mai muhimmanci da suke cikin Littafi Mai Tsarki. Duk wannan ɓangare ne na aikin ilimantarwa da ake yi a yau yadda ba a taɓa yi ba dā. Menene sakamakon haka? Kamar yadda aka annabta a Ishaya 2:2-4, ‘mutane da yawa,’ hakika fiye da miliyan shida daga dukan duniya, an ‘koyar da su ɗai-ɗai tafarkun Jehovah kuma suna tafiya cikin hanyoyinsa.’ A alamance, sun koyi su “bubbuge takubansu su zama garmuna, māsunsu kuma su zama lauzuna.” Sun samu salama da kwanciyar rai a wannan zamani na bala’i.
Kai Fa?
Ka yi ɗan bimbini bisa azaba da wahala da yasar da Ƙa’idar Ja-Gora ta kawo bisa ’yan Adam, tun tawaye a Adnin da Shaiɗan Iblis ya zuga. Jehovah ya nufa ya sake yanayin ba da daɗewa ba. Ta yaya? “Dalilin bayyanuwar Ɗan Allah ke nan, shi halaka ayyukan Shaiɗan.” (1 Yohanna 3:8) Wannan zai faru a cikin Mulkin Allah, a hannun mai hikima kuma wanda ya dace, Yesu Kristi, wanda ya koyar kuma ya rayu bisa Ƙa’idar Ja-Gora.—Zabura 37:9-11; Daniel 2:44.
Sarki Dauda na Isra’ila ta dā ya lura: “Dā yaro ni ke, yanzu kuwa na tsufa: amma ban taɓa gani an yar da mai-adalci ba, ko kuwa zuriyarsa suna roƙon abincinsu. Dukan yini yana aikin alheri, yana bada rance; zuriyarsa kuwa mai-albarka ce.” (Zabura 37:25, 26) Ba ka yarda ba cewa yawancin mutane a yau sun karɓa kuma suna kwace maimakon ‘aikin alheri, da ba da rance?’ A bayyane yake, bin Ƙa’idar Ja-Gora zai kai ga salama ta gaske da kuma kwanciyar rai, domin tana sa mutum bisa hanyar albarka a yau da kuma a nan gaba cikin Mulkin Allah. Mulkin Allah zai share dukan son kai da mugunta a duniya kuma ya sake wannan zamani na lalacacciyar sarauta ta mutane da sabon zamani da Allah zai yi. A lokacin, dukan mutane za su ji daɗin rayuwa bisa Ƙa’idar Ja-Gora.—Zabura 29:11; 2 Bitrus 3:13.
[Hotuna a shafi na 5]
Yesu ba koyar da Ƙa’idar Ja-Gora kawai ya yi ba amma ya kafa misali mafi kyau na yinta
[Hotuna a shafi na 7]
Bin Ƙa’idar Ja-Gora zai kai ga salama ta gaske da kwanciyar rai