Watchtower LABURARE NA INTANE
Watchtower
LABURARE NA INTANE
Hausa
Ɓ
  • Ā
  • ā
  • Ɓ
  • ɓ
  • ɗ
  • Ɗ
  • Ƙ
  • ƙ
  • ꞌY
  • ꞌy
  • LITTAFI MAI TSARKI
  • WALLAFE-WALLAFE
  • TARO
  • lfb darasi na 4 p. 16-p. 17 par. 2
  • Fushi Ya Jawo Kisan Kai

Babu bidiyo don wannan zabin

Yi hakuri, bidiyon na da dan matsala

  • Fushi Ya Jawo Kisan Kai
  • Darussa daga Littafi Mai Tsarki
  • Makamantan Littattafai
  • Ɗan Kirki, Da Kuma Mugun Ɗa
    Littafina na Labarun Littafi Mai Tsarki
  • A Ina ne Kayinu Ya Sami Matarsa?
    Amsoshin Tambayoyi Daga Littafi Mai Tsarki
  • ‘Shi da Yake Matacce Ne, Yana Jawabi Har Yanzu’
    Ka Yi Koyi Da Bangaskiyarsu
  • ‘Shi da Ya Ke Matacce Yana Jawabi Har Yanzu’
    Hasumiyar Tsaro Mai Shelar Mulkin Jehobah—2013
Darussa daga Littafi Mai Tsarki
lfb darasi na 4 p. 16-p. 17 par. 2
Kayinu ya yi fushi sa’ad da Habila ya mika hadaya ga Jehobah

DARASI NA 4

Kayinu Ya Kashe Habila

Adamu da Hauwa’u sun haifi yara da yawa bayan da aka kore su daga lambun Adnin. Kayinu ne yaronsu na farko, kuma shi manomi ne. Na biyun kuma mai suna Habila, yana kiwon dabbobi.

Wata rana sai Kayinu da Habila suka yi wa Jehobah hadaya. Ka san abin da hadaya take nufi? Wata irin kyauta ce da ake ba Allah. Jehobah ya karɓi hadayar Habila amma bai karɓi na Kayinu ba. Sai Kayinu ya yi fushi sosai. Jehobah ya ja kunnen Kayinu kuma ya gaya masa cewa idan bai bar fushin nan ba, zai yi wani abin da ba kyau. Amma Kayinu bai ji ba.

Maimakon haka, ya gaya wa Habila: ‘Ka zo mu je gona tare.’ Da suka je gonar kuma Kayinu ya ga ba kowa a wurin, sai ya kashe ƙaninsa Habila. Mene ne Jehobah ya yi? Jehobah ya hukunta Kayinu, kuma ya kore shi zuwa wani wuri mai nisa. Bai yarda Kayinu ya sake dawowa wurin ’yan’uwansa ba.

Kayinu ya zo wurin Habila a gona

Wane darasi ne za mu iya koya daga wannan labarin? Za mu iya yin fushi idan ba a yi mana abubuwan da muke so ba. Idan mun ga cewa mun soma yin fushi ko kuma idan wasu sun ga muna fushi kuma suka gaya mana mu daina, zai yi kyau mu daina fushin don kada mu yi laifi.

Da yake Habila ya ƙaunaci Jehobah kuma ya yi abin da yake da kyau, Jehobah ba zai taɓa mantawa da shi ba. Allah zai tayar da Habila a lokacin da aka mayar da duniya aljanna.

‘Ka je ku shirya da ɗan’uwanka, sa’an nan ka zo ka miƙa hadayarka.’​—Matta 5:24

Tambayoyi: Su waye ne yara biyu da Adamu da Hauwa’u suka fara haifa? Me ya sa Kayinu ya kashe ɗan’uwansa?

Farawa 4:​1-12; Ibraniyawa 11:4; 1 Yohanna 3:​11, 12

    Littattafan Hausa (1987-2026)
    Fita
    Shiga Ciki
    • Hausa
    • Raba
    • Wadda ka fi so
    • Copyright © 2026 Watch Tower Bible and Tract Society of Pennsylvania
    • Ka'idojin Amfani
    • Tsarin Tsare Sirri
    • Saitin Tsare Sirri
    • JW.ORG
    • Shiga Ciki
    Raba