Watchtower LABURARE NA INTANE
Watchtower
LABURARE NA INTANE
Hausa
Ɓ
  • Ā
  • ā
  • Ɓ
  • ɓ
  • ɗ
  • Ɗ
  • Ƙ
  • ƙ
  • ꞌY
  • ꞌy
  • LITTAFI MAI TSARKI
  • WALLAFE-WALLAFE
  • TARO
  • lfb darasi na 5 p. 18-p. 19 par. 5
  • Jirgin Nuhu

Babu bidiyo don wannan zabin

Yi hakuri, bidiyon na da dan matsala

  • Jirgin Nuhu
  • Darussa daga Littafi Mai Tsarki
  • Makamantan Littattafai
  • Nuhu Ya Gina Jirgi
    Littafina na Labarun Littafi Mai Tsarki
  • Babbar Rigyawa—Su Wane Ne Suka Yi Biyayya? Su Wane Ne Ba Su Yi Ba?
    Ka Saurari Allah Don Ka Rayu Har Abada
  • Ya Yi “Tafiya Tare da Allah”
    Hasumiyar Tsaro Mai Shelar Mulkin Jehobah—2013
  • Ya Yi “Tafiya Tare da Allah”
    Ka Yi Koyi Da Bangaskiyarsu
Dubi Ƙari
Darussa daga Littafi Mai Tsarki
lfb darasi na 5 p. 18-p. 19 par. 5
Nuhu da iyalinsa sun gina jirgi

DARASI NA 5

Jirgin Nuhu

A kwana a tashi, sai mutane suka soma yawa a duniya. Amma yawancinsu ba sa yin abu mai kyau. Har da wasu mala’iku ma da ke sama. Sun sauko daga sama zuwa duniya. Ka san dalilin da ya sa suka yi hakan? Domin su sami jiki irin na mutane kuma su auri mata.

Matan da mala’ikun suka aura sun haifi yara. Waɗannan yaran sun yi girma sosai kuma suka zama mugaye. Jehobah bai bari su ci gaba da yin mugunta ba. Ya ce zai halaka su da ambaliyar ruwa.

Nuhu da iyalinsa sun gina jirgi kuma suna shirya abinci

Amma akwai wani mutum da ba ya mugunta. Yana ƙaunar Jehobah sosai. Sunansa Nuhu. Shi da matarsa suna da yara uku. Sunayensu Shem da Ham da Japheth kuma dukansu sun yi aure. Jehobah ya gaya wa Nuhu cewa ya gina babban jirgin ruwa da ke kama da akwati da za su zauna a ciki don kada su mutu. Jehobah ya kuma gaya wa Nuhu cewa ya shigar da dabbobi da yawa cikin jirgin don kada su mutu.

Nan da nan sai Nuhu ya soma gina jirgin. Sun yi shekara hamsin kafin su gama aikin. Sun gina jirgin yadda Jehobah ya gaya musu. A lokacin, Nuhu ya gaya wa mutanen cewa Jehobah zai halaka su da ruwa idan ba su daina yin mugunta ba. Amma ba su ji ba.

Sa’ad da lokaci ya kai, sai Nuhu da iyalinsa suka shiga cikin jirgin. Bari mu ji abin da ya faru bayan haka.

“Kamar yadda aka yi a zamanin Nuhu, haka dawowar Ɗan Mutum za ta zama.”​—Matta 24:​37, Littafi Mai Tsarki

Tambayoyi: Me ya sa Jehobah ya ce zai halaka mugaye da ambaliyar ruwa? Mene ne Jehobah ya ce Nuhu ya yi?

Farawa 6:​1-22; Matta 24:​37-41; 2 Bitrus 2:5; Yahuda 6

    Littattafan Hausa (1987-2026)
    Fita
    Shiga Ciki
    • Hausa
    • Raba
    • Wadda ka fi so
    • Copyright © 2026 Watch Tower Bible and Tract Society of Pennsylvania
    • Ka'idojin Amfani
    • Tsarin Tsare Sirri
    • Saitin Tsare Sirri
    • JW.ORG
    • Shiga Ciki
    Raba