RAYUWAR KIRISTA
Za Ka Iya Wa’azi da Koyarwa!
Da farko Musa ya ga kamar ba zai iya aikin da Jehobah ya ba shi ba. (Fit 4:10, 13) Ka taɓa jin hakan? Kana nazarin Littafi Mai Tsarki da Shaidun Jehobah ne? Shin kana ganin ba za ka iya zuwa gida-gida kana wa’azi ba? Ko kai matashi ne da kake jin tsoron yin wa’azi a makaranta? Ko kana jin tsoron yin wa’azi ta waya ko a inda jama’a suke? Ka yi addu’a ga Jehobah kuma ka roƙe shi ya ba ka ruhu mai tsarki. (1Bi 4:11) Ka kasance da tabbaci cewa zai taimaka maka ka yi duk aikin da ya ba ka.—Fit 4:11, 12.
KU KALLI BIDIYON NAN KU ZAMA DA ƘARFIN ZUCIYA . . . MASU SHELA, SAI KU AMSA TAMBAYOYI NA GABA:
Wace matsala ce ’Yar’uwa Aoyama ta fuskanta?
Mene ne ya taimaka mata ta kasance da ƙarfin zuciya?—Irm 20:7-9
Ta yaya ta amfana sa’ad da ta faɗaɗa hidimarta?
Waɗanne matsaloli ne Jehobah zai taimaka maka ka magance su a wa’azi?