DARUSSA DAGA KALMAR ALLAH | KOLOSIYAWA 1-4
Ku Kawar da Halinku na Dā, Sai Ku Yafa Sabon Hali
Shin ka daina wasu halayen banza sa’ad da ka soma bauta wa Jehobah? Idan ka yi hakan, babu shakka Jehobah ya yi farin ciki sosai da canjin da ka yi. (Eze 33:11) Duk da haka, kana bukatar ka yi ƙoƙari don kar ka koma yin halayen nan da ka bari, amma ka ci gaba da zama mutumin kirki. Ka amsa tambayoyi na gaba don ka ga wuraren da kake bukatar yin gyara:
Shin ina riƙe mutanen da suka yi min laifi a zuci ne ko ina gafarta musu?
Ina yin haƙuri da mutane ko da ina sauri ko kuma na gaji?
Idan tunanin lalata ya shigo zuciyata, ina ci gaba da tunanin ne ko kuma ina daina tunanin da sauri?
Ina raina mutanen wasu ƙabilu ko wata ƙasa ne?
Na taɓa hasala ma wani kwanan nan ko kuma na yi masa baƙar magana?