DARUSSA DAGA KALMAR ALLAH | AYYUKAN MANZANNI 23-24
An Zarge Shi da Ta da Rikici da Kuma Tashin Hankali
Yahudawa da ke Urushalima sun “yi rantsuwa” cewa sai sun kashe Bulus. (A. M 23:12) Amma Jehobah yana son Bulus ya je Roma don ya yi wa’azi. (A. M 23:11) Da yaron ’yar’uwar Bulus ya ji ƙullin da ake yi, sai ya gaya wa Bulus kuma hakan ya sa ba a iya kashe shi ba. (A. M 23:16) Me wannan labarin ya koya maka game da . . .
duk wani ƙulli da za a yi don a hana cikar nufin Allah?
hanyoyin da Jehobah yake amfani da su don ya taimaka mana?
ƙarfin hali?