DARUSSA DAGA KALMAR ALLAH | MATTA 4-5
Darussan da Muka Koya Daga Huɗubar Yesu a kan Dutse
Shin kana marmarin karanta Kalmar Allah?
Wannan furucin “waɗanda suka san cewa suna bukatar ƙulla dangantaka da Allah” yana nufin “waɗanda suka san cewa suna bukatar ja-gorancin Allah.” (Mt 5:3, New World Translation) Za mu nuna muna son ja-gorancin Allah idan . . .
muna karanta Littafi Mai Tsarki kowace rana
muna yin shiri kuma muna halartar taronmu
muna karanta littattafanmu da wasu abubuwan da ake saka mana a dandalinmu idan da lokaci
muna kallon shirinmu a Tashar JW kowane wata
Ta yaya zan kyautata yadda nake karanta Kalmar Allah?