Bitar Makarantar Hidima ta Allah
Za a tattauna tambayoyin da ke gaba a Makarantar Hidima ta Allah a makon 28 ga Afrilu, 2014.
Mene ne ya taimaka wa Yusufu ya guji yin zina da matar Fotifa? (Far. 39:7-12) [3 ga Maris, w13 2/15 shafi na 4 sakin layi na 6; w07 11/1 shafi na 11 sakin layi na 16]
Ta yaya Yusufu ya kafa misali mai kyau ma waɗanda suke fuskantar rashin adalci da kuma matsaloli a yau? (Far. 41:14, 39, 40) [10 ga Maris, w04 6/1 shafi na 31 sakin layi na 6]
Me ya sa cin abinci tare da Ibraniyawa ya zama abin ƙyama ga Masarawa? (Far. 43:32) [17 ga Maris, w04 6/1 shafi na 31 sakin layi na 1]
Mene ne labarin Simeon da Lawi ya nuna game da ramuwar gayya? (Far. 49:5-7) [24 ga Maris, w10 6/15 shafi na 16 sakin layi na 8]
Mene ne za mu iya koya game da Jehobah a littafin Fitowa 3:7-10? [31 ga Maris, w09 4/1 shafi na 19 sakin layi na 3-6]
Mene ne Jehobah ya yi a zamanin Musa don ya cika wani fanni na ma’anar sunansa? (Fit. 3:14, 15) [31 ga Maris, w13 3/15 shafuffuka na 25-26 sakin layi na 5-6]
Bisa ga abin da ke Fitowa 7:1, ta yaya Musa ya zama kamar “Allah ga Fir’auna”? [7 ga Afrilu, w04 7/1 shafi na 26 sakin layi na 3]
Duk da cewa Isra’ilawa sun shaida ikon Jehobah a lokacin da ya ’yantar da su daga ƙasar Masar, wane irin hali ne suka nuna daga baya, kuma wane darasi ne hakan ya koya mana? (Fit. 14:30, 31) [14 ga Afrilu, w12 3/15 shafuffuka na 26-27 sakin layi na 8-10]
Me ya nuna cewa Allah yana kula da mata? (Fit. 20:12; 21:15, 17) [28 ga Afrilu, w12 10/1 shafi na 5 sakin layi na 1, 2]
Ta yaya Jehobah yake “kama ’ya’ya da muguntar ubanni”? (Fit. 20:5) [28 ga Afrilu, w04 7/1 shafi na 27 sakin layi na 1]