Bitar Makarantar Hidima ta Allah
Za a amsa waɗannan tambayoyi na gaba a Makarantar Hidima ta Allah a makon 31 ga Disamba, 2012. An saka kwanan watan da za a tattauna waɗannan bayanan domin ku yi bincike sa’ad da kuke shirya Makarantar Hidima ta Allah kowane mako.
1. Ta yaya annabcin da ke littafin Joel 2:1-10, 28 game da ƙwarin da suka kai hari ya cika? [5 ga Nuwamba, w07 11/1 shafi na 29, sakin layi na 1]
2. Ta yaya koyo game da Amos zai taimake mu idan muna jin cewa ba mu cancanta ba mu yi wa’azi? (Amos 7:14) [12 ga Nuwamba, w04 12/1 shafi na 8, sakin layi na 3]
3. Me ya sa Edomawa suka yi taurin kai kuma mene ne bai kamata mu manta ba? (Obad. 3, 4) [19 ga Nuwamba, w07 12/1 shafi na 8, sakin layi na 6]
4. Yaya Jehobah ya dakatar da nufinsa game da masifar da ya ce zai faru da mutanen Nineveh? (Yun. 3:8, 10) [19 ga Nuwamba, w07 12/1 shafi na 10, sakin layi na 1]
5. A “kwanaki na ƙarshe” ta yaya Jehobah yake ‘raba shari’a tsakanin ƙabilai dayawa, kuma ya raba tsakanin manyan al’ummai’? (Mik. 4:1-4) [26 ga Nuwamba, w07 12/1 shafi na 10, sakin layi na 7]
6. Ta yaya ne Nineveh ta zama kamar karuwa? (Nah. 3:4) [3 ga Disamba, w07 12/1 shafi na 13, sakin layi na 4]
7. Mene ne ma’anar maganar da ke Hagai 1:6, kuma wane darasi ne muka koya? [10 ga Disamba, w06 5/1 shafi na 9, sakin layi na 12-15]
8. Su waye aka haɗa cikin waɗanda Jehobah ya kira “mutanena”? (Zak. 2:11; 8:2) [17 ga Disamba, w10 3/15 shafi na 28, sakin layi na 19]
9. Ta yaya kalmomin da ke Zakariya 4:6, 7 suke ƙarfafa bayin Jehobah a yau? [17 ga Disamba, w07 12/1 shafi na 18, sakin layi na 7]
10. Bisa ga abin da aka faɗa a littafin Malakai 3:16, me ya sa bai kamata mu yi sanyin gwiwa a aminci ga Allah ba? [31 ga Disamba, br1-HA shafi na 31, sakin layi na 2]