Tsarin Ayyuka na Makon 12 ga Nuwamba
MAKON 12 GA NUWAMBA
Waƙa ta 66 da Addu’a
□ Nazarin Littafi Mai Tsarki na Ikilisiya:
cl shafi na 266 zuwa shafi na 269 da akwati (minti 30)
□ Makarantar Hidima ta Allah:
Karatun Littafi Mai Tsarki: Amos 1-9 (minti 10)
Na 1: Amos 3:1-15 (minti 4 ko ƙasa da hakan)
Na 2: Sa’ad da Allah Ya Amince a Canja Addini—td 2C (minti 5)
Na 3: Ta Yaya Za Mu Amfana Idan Mun Fahimci Zabura 51:17? (minti 5)
□ Taron Hidima:
Waƙa ta 68
Minti 10: Idan Wani Ya Ce: ‘Ba ku Gaskata da Yesu Ba.’ Ka tattauna tambayoyin da ke gaba da masu sauraro. Me ya sa mutane a yankinmu suke faɗin hakan? Waɗanne tambayoyi ne za a iya yin amfani da su don sanin abin da ke zuciyarsu? Wane sashen koyarwar Yesu ne wataƙila za su so? Waɗanne bayanai muke da su a babi na 4 na littafin nan Menene Ainihi Littafi Mai Tsarki Yake Koyarwa? ne za a iya yin amfani da su don ba da amsa? Ka gaya wa masu sauraro cewa za su iya karanta wa maigidan da ya ta da wannan hujjar manufar Hasumiyar Tsaro da ke shafi na biyu a cikin Hasumiyar Tsaro na kwanan nan. Ka sa a nuna yadda za a yi hakan.
Minti 10: Mene Ne Muka Koya? Tattaunawa. Ka sa a karanta Markus 1:16-20. Ka tattauna da masu sauraro yadda darussan da za mu koya daga waɗannan ayoyin za su iya taimaka mana a wa’azi.
Minti 10: “Ku Ci Moriyar Aikinku.” Tambayoyi ana ba da amsoshi.
Waƙa ta 98 da Addu’a