Ayyuka na Makon 20 ga Fabrairu
MAKON 20 GA FABRAIRU
Waƙa ta 37 da Addu’a
□ Nazarin Littafi Mai Tsarki na Ikilisiya:
cl shafi na 138 zuwa 141, sakin layi na 8 (minti 25)
□ Makarantar Hidima ta Allah:
Karatun Littafi Mai Tsarki: Ishaya 58-62 (minti 10)
Na 1: Ishaya 61:1-11 (minti 4 ko ƙasa da hakan)
Na 2: Me Ya Sa Keɓe Kai Alamar Ƙauna Ce da Bangaskiya? (minti 5)
Na 3: Sanin Ingancin Allah—td 23C (minti 5)
□ Taron Hidima:
Waƙa ta 87
Minti 10: Sanarwa. Ka ambata littattafan da za a ba da a watan Maris, kuma ka sa a yi gwaji guda.
Minti 10: Mene Ne Muka Koya? Tattaunawa. Ka sa a karanta Zabura 63:3-8 da Markus 1:32-39. Ku tattauna yadda waɗannan nassosi za su taimaka mana a hidimarmu.
Minti 15: “Za a Soma Kamfen na Gayyatar Mutane Zuwa Taron Tuna Rasuwar Yesu a Ranar 17 ga Maris.” Tambayoyi ana ba da amsoshi. Idan da akwai takardar gayyata, ka sa a rarraba wa dukan ’yan’uwa kuma ku tattauna abin da ke ciki. Sa’ad da kuke tattauna sakin layi na 2, ka sa a yi ɗan gwaji da zai nuna yadda za a yi gayyatar. Sa’ad da ake tattauna sakin layi na 3, ka gayyaci mai kula da hidima ya faɗi yadda za a gayyaci mutane a dukan yankin.
Waƙa ta 8 da Addu’a