Bitar Makarantar Hidima Ta Allah
Za a amsa waɗannan tambayoyi na gaba a Makarantar Hidima Ta Allah a makon 26 ga Disamba, 2011.
1. Mene ne ya kamata ka yi idan kana yin abin da ka san ba shi da kyau a ɓoye? [w10 11/15 shafi na 6 sakin layi na 18]
2. Mene ne kalmar nan “banza” take nufi? (M. Wa 1:2, 3) [w08 4/15 shafi na 21 sakin layi na 4]
3. A wane yanayi ne aiki tuƙuru yake jawo baƙin ciki da kishi? (M. Wa 4:4) [w06 11/1 shafi na 30 sakin layi na 8]
4. “Cika yin adalci” yana ɗauke da wane haɗari? (M. Wa. 7:16) [w10 10/15 shafi na 9 sakin layi na 8-9]
5. Ta yaya Waƙar Waƙoƙi 2:7 ta nuna cewa waɗanda suke son yin aure za su yi hikima idan ba su yi garaje wajen zaɓan abokin aure ba? [w06 12/1 shafi na 26 sakin layi na 6]
6. Mene ne ma’anar laɓɓan ’yar Shulem da ke ɗigar da saƙar zuma da kuma ‘zuma da nono da ke ƙarƙashin harshenta’? (W. Waƙ. 4:11) [w06 12/1 shafi na 27 sakin layi na 1]
7. Me ya sa Jehobah ya ceci mugun Sarki Ahaz? (Isha. 7:3, 4) [w06 12/1 shafi na 28 sakin layi na 9]
8. Me ya sa ya dace iyaye su yi bimbini a kan misalin Yesu? (Isha. 9:6, 7) [w05 7/1 shafi na 9 sakin layi na 7]
9. Wane halin Iblis ne ya bayyana a kalamin da ke rubuce a Ishaya sura 14? [w06 2/1 shafi na 8 sakin layi na 1]
10. A wane lokaci ne Yesu ya karɓi ‘makullin gidan Dauda,’ kuma ta yaya yake amfani da makullin? (Isha. 22:22) [w09 1/15 shafi 31 sakin layi na 2]