Tsarin Ayyuka na Makon 9 ga Mayu
MAKON 9 GA MAYU
Waƙa ta 58 da Addu’a
□ Nazarin Littafi Mai Tsarki na Ikilisiya:
bh babi na 18 sakin layi na 20-25 da akwati (minti 25)
□ Makarantar Hidima ta Allah:
Karatun Littafi Mai Tsarki: Zabura 1-10 (minti 10)
Na 1: Zabura 7:1-17 (minti 4 ko ƙasa da hakan)
Na 2: Littafi Mai Tsarki Hurarriyar Kalmar Ce Daga Allah—td 30A (minti 5)
Na 3: Dalilin da Ya Sa Yesu Ya Yi wa Mutumin da Ya Kira Shi “Malam Managarci” Gyara—Mar. 10:17, 18 (minti 5)
□ Taron Hidima:
Waƙa ta 4
Minti 5: Sanarwa.
Minti 10: Wa Kake wa Biyayya, Allah ko kuma ’Yan Adam. (A. M. 5:29) Tattaunawa da aka ɗauko daga Hasumiyar Tsaro ta 1 ga Janairu 2006, shafi na 11. Bayan ka tattauna kowanne labari ka gayyaci masu sauraro su yi kalami a kan darussan da suka koya.
Minti 10: Za Ka Iya Hidimar Majagaba na Ɗan Lokaci a Lokacin Hutu? Tattaunawa. Ka ɗan yi bitar shafuffuka na 112-113 na littafin nan Organized To Do Jehovah’s Will, kuma ka faɗi bukatun. Ka gayyaci waɗanda suka yi amfani da lokacin hutu daga aiki ko makaranta don yin hidimar majagaba na ɗan lokaci su faɗi albarkar da suka more.
Minti 10: “Ku Bari Haskenku Shi Haskaka.” Tambayoyi ana ba da amsoshi. Ka gayyaci masu sauraro su faɗi labarinsu na yadda hali mai kyau ya buɗe zarafin ba da shaida.
Waƙa ta 93 da Addu’a