Rahotannin Hidimar Fage
Masu shela daga wata ikilisiya da ke Legas sun tafi yin hidima a yanki da ba a sanya wa kowa ba a ƙauyen Ala da Idowa a jihar Ogun. Sun samu sakamako mai kyau. Alal misali, sun ga wata mata a yankin da ta naƙasa da ba ta iya tafiya ba sanadiyyar ciwon shan inna. Bayan sun karanta mata alkawarin Littafi Mai Tsarki cewa naƙasassu za su yi tafiya, ta ce: ‘Ba a taɓa ƙarfafa ni haka ba tun lokacin da nake da wannan matsalar. Na gaskata da wannan alkawarin. Amma tun da yake za ku tafi kuma ba ku da wurin taro a nan, wa zai sake koya mini irin wannan abin kuma? Wa zai ƙarfafa ni kuma? Don Allah kada ku tafi, kada ku bar ni.’ Za ku iya shirya harkokinku don ku yi wa irin waɗannan mutane wa’azi?