Ka Tuna?
Ka ji daɗin karanta talifofin Hasumiyar Tsaro na kwanan bayan nan? Ka ga ko za ka iya amsa tambayoyi na gaba:
• A wane azanci ne Allah zai sa ka yi arziki?
A dā, Jehobah ya albarkaci wasu, kamar su Ibrahim da Sulemanu da dukiya. Amma arziki da Kiristoci suke matuƙar bukata kuma Allah zai taimaka musu su samu, sun ƙunshi bangaskiya, salama, gamsuwa, da farin ciki.—10/1, shafuffuka na 3-7.
• Wane darasi za mu iya koya daga yadda Yesu ya ceci Bitrus sa’ad da yake nitsewa cikin teku? (Mat. 14:28-31)
Idan muka lura cewa wani ɗan’uwa yana rashin bangaskiya, a alamance muna iya miƙa hannunmu kuma mu taimaka masa ya samu ƙarin bangaskiya.—9/15, shafi na 8.
• Wace sadaukarwa ce Jehobah ya yi don ya cece mu?
Jehobah ya jimre sa’ad da ake gana wa Ɗansa azaba kuma aka yi masa ba’a. Kuma kamar yadda Ibrahim ya nuna sa’ad da ya kasance a shirye ya miƙa ɗansa, Jehobah ya jimre sa’ad da aka kashe Ɗansa a matsayin wanda ya yi laifi.—9/15, shafuffuka na 28-29.
• Wane darasi ne Misalai 24:27 ta koya mana game da ‘gina gida’?
Ya kamata saurayi da yake son ya yi aure ya yi shiri don wannan hakki. Wannan ya ƙunshi kasancewa a shirye ya yi tanadin abin biyan bukata ga iyalinsa kuma ya zama shugaba na ruhaniya na iyalin.—10/15, shafi na 12.
• Ta yaya Jehobah da Yesu suka kafa mana misali mai kyau wajen nuna halin kirki?
Duk da cewa Jehobah yana da matsayi mai girma, yana bi da mutane cikin alheri da kuma daraja. A yare na asali, sa’ad da yake magana ga Ibrahim da Musa, Jehobah ya yi amfani da kalmar Ibrananci da ke sa umurni ya zama kamar “roƙo.” (Far. 13:14; Fit. 4:6) Allah ya saurari mutane. (Far. 18:23-32) Yesu ma ya yi hakan, kuma yana shirye ya taimaka wa waɗanda suke kusa da shi, sau da yawa ya yi amfani da sunayensu.—11/15, shafi na 25.