Gabatarwar Sashe na 12
Yesu ya koyar da mutane game da Mulkin Allah. Ya kuma koyar da su cewa su yi addu’a a tsarkake sunan Allah, Mulkinsa ya zo kuma a yi nufinsa a duniya. Idan kana da yara, ka bayyana musu abin da addu’ar nan take nufi. Yesu bai bar Shaiɗan ya hana shi kasancewa da aminci ba. Yesu ya zaɓi manzanninsa kuma suka zama mutanen da aka fara zaɓa don su yi sarauta da shi a sama. Ka lura da himmar da Yesu ya nuna don bauta ta gaskiya. Yana so ya taimaka wa mutane shi ya sa ya warkar da marasa lafiya, ya ta da matattu da kuma ciyar da mayunwata. Mu’ujizojin da Yesu ya yi sun nuna abin da Mulkin Allah zai yi wa ’yan Adam a nan gaba.