Ƙarin Bayani
b Matta ya bayyana cewa baƙin “sun buɗe dukiyarsu” sai suka ba Yesu zinari, lubba, da jawul. Abin sha’awa, wataƙila waɗannan tsaraba masu tsada sun zo ne a daidai lokaci, tun da ba da daɗewa ba bayan hakan iyalin Yesu waɗanda talakawa ne sun yi gudun hijira.—Matta 2:11-15.