Watchtower LABURARE NA INTANE
Watchtower
LABURARE NA INTANE
Hausa
Ɓ
  • Ā
  • ā
  • Ɓ
  • ɓ
  • ɗ
  • Ɗ
  • Ƙ
  • ƙ
  • ꞌY
  • ꞌy
  • LITTAFI MAI TSARKI
  • WALLAFE-WALLAFE
  • TARO
  • w06 8/1 p. 27
  • Tambayoyi Daga Masu Karatu

Babu bidiyo don wannan zabin

Yi hakuri, bidiyon na da dan matsala

  • Tambayoyi Daga Masu Karatu
  • Hasumiyar Tsaro Mai Shelar Mulkin Jehobah—2006
  • Makamantan Littattafai
  • “Ina Misalin Zurfin . . . Hikimar Allah!”
    Ka Kusaci Jehobah
  • Hikima Tana Kira da Babban Murya
    Hasumiyar Tsaro Mai Shelar Mulkin Jehobah (Na Nazari)—2022
  • “Hikima Mai-Fitowa Daga Bisa” Tana Aiki Kuwa A Rayuwarka?
    Ka Kusaci Jehobah
Hasumiyar Tsaro Mai Shelar Mulkin Jehobah—2006
w06 8/1 p. 27

Tambayoyi Daga Masu Karatu

Ta yaya muka sani cewa yadda aka kwatanta hikima a Misalai 8:22-31 ya shafi Yesu Kristi ne kafin ya zama mutum?

Kwatanci na hikima a cikin littafin Misalai ta ce: “Ubangiji ya yi ni tun farkon hanyarsa, tun gaban ayyukansa na dā . . . Tun duwatsu ba su kafu ba, tun gaban tuddai aka fito da ni . . . Lokacin da ya shirya sammai ina nan . . . Sa’annan ina nan wurinsa, gwanin mai-aiki ne, kowace rana ni ne abin daularsa, kullum ina farinciki a gabansa, . . . daulata tana wurin ’yan adam.”

Wannan nassi ba ya magana kawai a kan hikima ta Allah ko kuma hikimar da ba a gani ba. Me ya sa? Saboda hikima da aka kwatanta a nan an “yi” ko halicce ta ne a farkon hanyar Jehobah. Jehobah Allah yana wanzuwa koyaushe kuma a koyaushe yana da hikima. (Zabura 90:1, 2) Hikimarsa ba ta da mafari; kuma ba a halicce ta ba. Ba a kuma ‘fito da ita ba.’ Bugu da ƙari, irin wannan hikima an ce tana magana kuma tana aiki, wannan yana wakiltar mutum.—Misalai 8:1.

Littafin Misalai ya ce tun da daɗewa hikima tana tare da Jehobah, Mahalicci, a matsayin “gwanin mai aiki.” Babu shakka, wannan ya shafi Yesu. Kafin ya zo duniya, Yesu ya yi aiki tare da Jehobah, shi ya sa kalmar Allah ta ce: “Shi ne kuwa gaba da dukan abu, a cikinsa kuwa dukan abu suna harhaɗe.”—Kolossiyawa 1:17; Ru’ya ta Yohanna 3:14.

Ya dace a ce Ɗan Allah ne hikima, tun da shi ne ya bayyana manufar Jehobah mai kyau da kuma dokarsa. Kafin ya zama mutum, Yesu Kalmar Allah ne, ko kuma Kakakinsa. (Yohanna 1:1) An kwatanta shi a matsayin “ikon Allah, da hikimar Allah.” (1 Korinthiyawa 1:24, 30) Wannan kwatanci ne mai kyau wanda aka yi wa Ɗan Allah, wanda ƙaunar da yake da shi ga mutane ya motsa shi ya ba da ransa fansa don mutane!—Yohanna 3:16.

[Hoto a shafi na 27]

Kafin “duwatsu . . . aka fito da ni”

    Littattafan Hausa (1987-2026)
    Fita
    Shiga Ciki
    • Hausa
    • Raba
    • Wadda ka fi so
    • Copyright © 2026 Watch Tower Bible and Tract Society of Pennsylvania
    • Ka'idojin Amfani
    • Tsarin Tsare Sirri
    • Saitin Tsare Sirri
    • JW.ORG
    • Shiga Ciki
    Raba