Gabatarwar Sashe na 13
Yesu ya zo duniya don ya mutu a madadin ’yan Adam. Duk da cewa ya mutu, ya yi nasara da duniya. Jehobah ya cika alkawarinsa kuma ya ta da Ɗansa daga matattu. Har Yesu ya mutu, ya taimaka wa mutane kuma ya gafarta musu sa’ad da suka yi kuskure. Ya bayyana ga mabiyansa bayan ya tashi daga mutuwa. Ya koya musu yadda za su yi aiki mai muhimmancin da ya ba su. Idan ku iyaye ne, ku taimaka wa yaranku su san cewa mu ma muna sa hannu a wannan aikin a yau.