ABIN DA LITTAFI MAI TSARKI YAKE NUFI
Yesu “Ya Koyi Yin Biyayya”
Yesu ya yi shekaru aru-aru yana yi wa Jehobah biyayya. (Yoh. 8:29) To, me ya sa Littafi Mai Tsarki ya ce: “Ya koyi yin biyayya ta hanyar azabar da ya sha”?—Ibran. 5:8.
Saꞌad da Yesu yake duniya, ya fuskanci yanayoyin da babu irinsu a sama. Alal misali, iyayensa suna ƙaunar Jehobah amma su ajizai ne. (Luk. 2:51) Ya sha wahala a hannun mugayen shugabannin addinai da kuma masu mulki. (Mat. 26:59; Mar. 15:15) Ƙari ga haka, an azabtar da shi kafin ya mutu. Littafi Mai Tsarki ya ce: “Ya ƙasƙantar da kansa ta wurin yin biyayya, biyayyar da ta kai shi har ga mutuwa.”—Filib. 2:8.
Waɗannan abubuwan sun sa Yesu ya koyi yin biyayya a hanyar da bai taɓa yi ba a sama. Hakan ya sa ya zama wanda ya dace ya zama Sarki da kuma Babban Firist domin ya fahimci yanayinmu da kyau. (Ibran. 4:15; 5:9) Bayan Yesu ya koyi biyayya daga azabar da ya sha, Jehobah ya ƙara daraja shi, kuma ya yi amfani da shi a hanyoyi da dama. Mu ma Jehobah zai ƙara daraja mu idan mun ci-gaba da yin biyayya ko da muna shan wuya.—Yak. 1:4.