RAYUWAR KIRISTA
Jehobah Yana Kāre Mutanensa
Idin Ƙetarewa na farko da aka yi yana da muhimmanci sosai. Da Fir’auna ya ga cewa ɗan farinsa ya mutu a daren, sai ya kira Musa ya ce: “Tashi! Ku fita ku bar mutanena, ku da jama’arku Isra’ila! Ku tafi ku yi wa Yahweh sujada, kamar yadda kuka faɗa.” (Fit 12:31) Wannan abin da Jehobah ya yi ya nuna cewa yana kāre mutanensa.
Idan muka bincika tarihin Shaidun Jehobah a yau, za mu gane cewa a kullum Jehobah yana ja-gorar mutanensa kuma yana kāre su. An nuna hakan a wurin adana kayayyakin tarihi da ke hedkwatarmu mai jigo, “A People for Jehovah’s Name.”
KU KALLI BIDIYON NAN ZAGAYA WURIN ADANA KAYAKIN TARIHI: “A PEOPLE FOR JEHOVAH’S NAME,” SA’AN NAN KU AMSA TAMBAYOYI NA GABA:
Wane abu ne Ɗaliban Littafi Mai Tsarki suka yi amfani da shi a farkon 1914 don mutane su ƙara gaskata da Littafi Mai Tsarki, kuma ta yaya suka yi nasara?
Waɗanne matsaloli ne suka fuskanta a 1914 da 1918, kuma me ya nuna cewa Jehobah ne yake wa ƙungiyarmu ja-gora?
Ta yaya bayin Jehobah suka jimre sa’ad da maƙiyansu suka yi adawa da su?
Wane ƙarin haske ne bayin Jehobah suka samu a shekara ta 1935, kuma ta yaya hakan ya shafe su?
Idan ka taɓa zuwa wurin adana kayayyakin tarihin nan, me ka gani da ya tabbatar maka cewa Jehobah ne yake ja-gorar mutanensa kuma yana kāre su?