DARUSSA DAGA KALMAR ALLAH | AYYUKAN MANZANNI 17-18
Ku Yi Koyi da Yadda Bulus Ya Yi Wa’azi da Kuma Koyarwa
Ta yaya za mu bi misalin manzo Bulus?
Mu yi amfani da Littafi Mai Tsarki don mu ba da hujja ga abin da muka faɗa wa mutane kuma mu bayyana musu yadda za su fahimta
Mu riƙa yin wa’azi a inda za mu sami mutane
Kada mu kushe imanin mutane amma mu yi amfani da shi don mu ja hankalinsu ga abin da muke so mu koya musu