19-25 ga Nuwamba
AYYUKAN MANZANNI 4-5
Waƙa ta 73 da Addu’a
Gabatarwar Taro (minti 3 ko ƙasa da hakan)
DARUSSA DAGA KALMAR ALLAH
“Sun Ci gaba da Koyar da Kalmar Allah da Ƙarfin Zuciya”: (minti 10)
A. M 4:5-13—Bitrus da Yohanna “marasa ilimi ne” kuma talakawa, amma ba su ji tsoron kāre imaninsu a gaban mahukunta, da marubuta ba (mwbr18.11-HA an ɗauko daga w08 9/1 akwatin da ke shafi na 15; w08 5/15 30 sakin layi na 6)
A. M 4:18-20—Bitrus da Yohanna sun ƙi su daina yin wa’azi duk da cewa an hana su yin hakan
A. M 4:23-31—Kiristocin ƙarni na farko sun roƙi Allah ya ba su ruhu mai tsarki don su yi ƙarfin zuciya (mwbr18.11-HA an ɗauko daga it-1 128 sakin layi na 3)
Neman Abubuwa Masu Tamani: (minti 8)
A. M 4:11—Ta yaya Yesu ya zama dutse “mafi amfani a gini”? (mwbr18.11-HA an ɗauko daga it-1 514 sakin layi na 4)
A. M 5:1—Me ya sa Hananiya da matarsa Safiratu suka sayar da wasu daga cikin dukiyarsu? (w13 5/1 9 sakin layi na 4)
Mene ne karatun Littafi Mai Tsarki na wannan makon ya koya maka game da Jehobah?
Waɗanne darussa ne kuma ka koya a karatun Littafi Mai Tsarki na wannan makon?
Karatun Littafi Mai Tsarki: (minti 4 ko ƙasa da hakan) A. M 5:27-42
KA YI WA’AZI DA ƘWAZO
Haɗuwa ta Fari: (minti 2 ko ƙasa da hakan) Ka bi bayanin da ke Yadda Za Mu Yi Wa’azi. Mutumin ya ba da hujja ta ƙin jin wa’azi da mutanen yankin suka saba bayarwa.
Komawa Ziyara ta Farko: (minti 3 ko ƙasa da hakan) Ka bi bayanin da ke Yadda Za Mu Yi Wa’azi. Mutumin ya ce maka shi ba Kirista ba ne.
Bidiyon Komawa Ziyara ta Biyu: (minti 5) Ka nuna bidiyon kuma ku tattauna shi.
RAYUWAR KIRISTA
“Albarkun Wa’azi da Amalanke a Faɗin Duniya”: (minti 15) Tattaunawa da mai kula da hidima zai yi. Ka nuna bidiyon. Idan kuna yin wa’azi da teburi ko kuma amalanke a ikilisiyarku, ka kawo teburin ko amalanken a kan dakalin magana don masu sauraro su ga yadda yake. Ka kuma bayyana yadda kuke yin hakan a ikilisiyarku. Idan da sauran lokaci, ka ba da wani labari mai daɗi game da hakan ko kuma ka sa a gwada abin da ya faru. Ka bayyana wa masu sauraro yadda su ma za su iya yin hakan.
Nazarin Littafi Mai Tsarki na Ikilisiya: (minti 30) lv babi na 16 sakin layi na 1-8
Bita da Abin da Za A Tattauna Mako Mai Zuwa (minti 3)
Waƙa ta 64 da Addu’a