DARUSSA DAGA KALMAR ALLAH | AYUBA 38-42
Yin Addu’a a Madadin Wasu Yana Faranta wa Jehobah Rai
Jehobah ya bukaci Ayuba ya yi addu’a a madadin Eliphaz da Bildad da kuma Zophar
42:7-10
Jehobah ya gaya wa Eliphaz da Bildad da kuma Zophar cewa su je wurin Ayuba don su yi hadayar ƙonawa
Jehobah ya bukaci Ayuba ya yi addu’a a madadinsu
Ayuba ya sami albarka bayan ya yi addu’a a madadinsu
Jehobah ya albarkaci Ayuba sosai don bangaskiya da kuma jimirinsa
42:10-17
Jehobah ya kawar da matsalar Ayuba kuma ya sa ya sami sauƙi
Abokan Ayuba da danginsa sun ƙarfafa shi don wahalar da ya sha
Jehobah ya maido wa Ayuba ninki biyu na arzikinsa da ya yi hasara
Bayan haka, Ayuba da matarsa sun sake haifan yara goma
An daɗa wa Ayuba shekaru 140 kuma hakan ya ba shi damar ganin jikokinsa har tsara huɗu