Sanarwa
◼ Littattafan da za mu ba mutane a watan Satumba da Oktoba: Mujallun Hasumiyar Tsaro da Awake! Nuwamba da Disamba: Ka ba da ɗaya cikin warƙoƙin nan: Za Ka so ka San Amsoshin Waɗannan Tambayoyin?, Matattu Za Su Sake Rayuwa Kuwa?, Mene ne Ra’ayinka Game da Littafi Mai Tsarki?, Mene ne Ra’ayinka Game da Nan Gaba?, Mene ne Ke Kawo Farin Ciki a Iyali?, Wane ne Ainihi Yake Iko da Duniya?, Wahala Za Ta Ƙare Kuwa?
◼ A shekara ta 2016, za a ba da jawabi na musamman na lokacin Tuna Mutuwar Yesu a makon 28 ga Maris. Za a sanar da jigon jawabin a nan gaba. Ikilisiyoyin da ke da taron da’ira a wannan makon ko kuma ziyarar mai kula da da’ira su ba da jawabin a mako na gaba. Kada a ba da jawabin kafin ranar 28 ga Maris.