WAƘA TA 162
Koyo don In San Allahna
1. Dukanmu na bukatar
Mu san nufin Jehobah.
Muna so mu yi rayuwa
Yadda Allah ke so.
Allah ya nuna mana
Nufinsa a Kalmarsa.
Kalmomin da ke cikinta
Na kwantar min da rai.
(AMSHI)
Yabi Jehobah kullum,
Bi hanyarsa, yi biyayya.
Zan ba Jehobah raina,
Zan dogara da shi.
Zan yi ta koyo,
In san Allahna.
2. Zan ɗau lokaci sosai
In riƙa yin tunani
A kan gaskiyar da na gano
A cikin Kalmarka.
Duk wanda bai san ka ba
Ya Allah taimake shi,
Don ya sami kwanciyar rai
Da rayuwa mai kyau.
(AMSHI)
Yabi Jehobah kullum,
Bi hanyarsa, yi biyayya.
Zan ba Jehobah raina,
Zan dogara da shi.
Zan yi ta koyo,
In san Allahna.
Yabi Jehobah kullum,
Bi hanyarsa, yi biyayya.
Zan ba Jehobah raina,
Zan dogara da shi.
Zan yi ta koyo,
In san Allahna.
Yabi Jehobah kullum,
Bi hanyarsa, yi biyayya.
Zan ba Jehobah raina,
Zan dogara da shi.
Zan yi ta koyo,
In san Allahna.
(Ka kuma duba Zab. 1:1, 2; 112:1; 119:97; Isha. 40:8; Mat. 5:6; 16:24; 2 Tim. 4:4)