WAƘA TA 39
Mu Yi Suna Mai Kyau a Wurin Allah
Hoto
(Mai-Wa’azi 7:1)
1. Duk rayuwarmu, A kullum muna so
Mu riƙa yi wa Jehobah biyayya.
In muna yin abin Da Allah yake so,
Za mu faranta Wa Allah rai.
2. Shaiɗan ya fi so Mu nemi ɗaukaka,
Har da arziki, A wannan duniyar.
Amma duk wofi ne, In mun so duniya,
Ba za mu sami Albarka ba.
3. Muna so Allah Ya amince da mu
Domin mu sami Rai na har abada.
Mu dogara da shi, Mu kāre sunansa,
Kuma mu riƙe Amincinmu.
(Ka kuma duba Far. 11:4; Mis. 22:1; Mal. 3:16; R. Yoh. 20:15.)