Gabatarwar Sashe na 14
Kiristoci a ƙarni na farko sun yaɗa bishara game da Mulki a wurare da yawa. Yesu ya nuna musu wurin da za su yi wa’azi kuma ya taimaka musu su iya yi wa mutane wa’azi a yarensu. Jehobah ya sa sun kasance da gaba gaɗi kuma ya ba su ƙarfi su jimre duk tsanantawar da aka yi musu.
Yesu ya saukar wa manzo Yohanna da wahayi da ya nuna ɗaukakar Allah. A wani wahayi, manzon ya ga yadda Mulkin Allah ya halaka Shaiɗan da kuma mabiyansa har abada. Ya ga Yesu da kuma mutane 144,000 suna sarauta. Ƙari ga haka, Yohanna ya ga duniya ta zama aljanna, mutane suna zaman lafiya kuma suna bauta wa Jehobah cikin haɗin kai.