Gabatarwar Sashe na 7
A wannan sashen, an ba da labarin Sarki Saul da kuma Dauda. Labarin da aka bayar abubuwa ne da suka faru wajen shekaru 80. Da farko, Saul ya yi wa Allah biyayya amma daga baya, ya daina bin umurnan Jehobah. Hakan ne ya sa Jehobah ya ƙi shi kuma ya sa Sama’ila ya naɗa Dauda a matsayin sarkin da zai mulki Isra’ilawa. Ɗan Saul mai suna Jonathan ya san cewa Dauda ne Jehobah ya zaɓa, kuma ya ci gaba da riƙe amincinsa ga Dauda. Dauda ya yi zunubi mai tsanani amma ya amince da gyarar da Jehobah ya yi masa. Idan kana da yaro, ka taimaka masa ya ga muhimmancin bin ja-gorancin Allah a koyaushe.